Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Ribas Omoni Nnamdi ya bayyana wa PREMIUM TIMES cewa an harbe mutane hudu a lokacin zabe a karamar hukumar Andoni.
Kakakin jam’iyyar APC a jihar Senibo Finebone ya bayyana cewa wasu tsageran jam’iyyar PDP sun harbe wani jigon jam’iyyar APC Mowan Etete.
Finebone ya kuma kara da cewa tsageran sun kuma bindige wasu ‘yan uwan sa biyu sannan da wani jami’in jam’iyyar APC mai suna Ignatius.
” Duk wannan abin tashin hankalin ya faru ne a karamar hukumar shugaban jam’iyyar PDP Prince Uche Secondus wato Andoni.”
Nnamdi ya ce rundunar ta dauki matakan samar da zaman lafiya a karamar hukumar sannan har sun fara gudanar da bincike domin kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika.
Kafin ranar zabe rundunar ‘yan sandan jihar ta bayyana cewa ta kammala shiri tsaf domin ganin ta hana tashin hankali da rikici da aka saba samu a jihar a duk lokacin zabe.