A rumfar zaben da tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido ya kada kuri’a jam’iyyar PDP ce ta yi Nasara.
Sule Lamido ya yi zabe mazabar sa dake Bamaina C karamar hukumar Birnin Kudu.
A sakamakon zaben shugaban kasa jam’iyyar PDP ta sami kuri’u 259 sannan APC 20
Zaben sanatoci kuwa PDP ta ja kuri’u 278 , APC 6
Sakamakon majalisar tarayya kuma na kasa PDP ta samu kuri’u 267, APC 17.
Discussion about this post