Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana cewa akalla na’urar tattance masu jefa kuri’a 4,695 ne suka kone kurmus a ofishin ta da ke jihar Anambra.
Wutar wadda ta tashi jiya Talata, ta faru ne kwana biyu bayan tashin wuta a ofishin INEC da ke karamar hukumar Qua’an Pam ta jihar Filato, mako guda kuma bayan tashin wata wutar a wani ofishin na INEC a daya daga cikin kananan hukumomin jihar Abia.
Daraktan Yada Labarai da wayar da kai na INEC, Festus Okoye ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar.
PREMIUM TIMES ta rigaya ta buga labarin na yadda kwantina biyu dauke da na’urar tantance masu jefa kuri’a ta ci wuta a hedikwatar INEC da ke Awka.
Wannan ce gobara ta uku a cikin kwanaki 12 a ofisoshin INEC daban-daban a fadin kasar nan.
INEC ta ce wannan koma-baya ne wajen gudanar da zabe a jihar Anambra. Sai dai kuma ta ce za ta gaggauta kalato wasu na’urorin tantance masu zaben daga wasu jihohi domin a cike gurabun wadanda suka kone a jihar Anambra.
INEC ta ce ta na da yakinin cewa za a gudanar da zabe a jihar Anambra a rana daya da sauran jihohin kasar nan.
Hukumar ta kuma sanar wa jami’an ‘yan sanda gobarar, inda ta kara da cewa ta jiran sakamakon rahoton ‘yan sanda.
Discussion about this post