Bello Mandiya, Ahmed Babba-Kaita da Kabir Barkiya na jam’iyyar APC duk sun lashe zabukan kujerun sanata na shiyyoyin su da aka yi ranar Asabar a jihar Katsina.
Babban mai tattara Hukumar zabe ta sanar da wannan sakamakon ne a o ta dake Daura, Katsina da Funtua.
A Katsina ta Kudu APC ta sami kuri’u 433,139, PDP kuma ta sami 158,081.
APC ta sami kuri’u 339,438, PDP ta sami kuri’u 127,529 a Katsina ta Arewa.
A Katsina ta tsakiya kuwa APC ta sami kuri’u 340,800, PDP 124,372.