Idan ba a mata ba a yau Talata ne kungiyar hadin kai da zaman lafiya wanda tsohon shugaban Kasa Abdussalami Abubakar ke jagoranta ta shirya taron saka hannu a yarjejeniyar zaman lafiya ga jam’iyyun kasar nan.
Shi dai irin wannan yarjejeniya akan yi shi ne idan zabe ya tunkaro inda gaggan ‘yan takara kan hadu wuri daya su rattaba hannu a wannan takarda da fatan a yi zabe lafiya.
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya halarci wannan taro kuma ya rattaba hannu a wannan yarjejeniya.
Sai dai kuma babban abokin hamayyar sa kuma dan takarar shgabancin kasa a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar bai halarci wannan taro ba.
Da muka ne mi ji daga bakin kakakin sa, Ya ce Atiku bashi da masaniyar wannan taro da aka yi da karfe uku na rana.