Wakilan Kungiyar Malaman Jami’ao’i ta Kasa, ASUU, sun fice daga taron neman yadda za a shawo kan malaman su janye yajin aiki da suka fara tun farkon watan Nuwamba.
Sun fice wa tawagar wakilan da Gwamnatin Tarayya ta tura din ne a karkashin Ministan Kwadago da Ma’aikata, Chris Ngige, a dakin taron jiya Litinin a Abuja.
Sau shida kenan ana zama tsakanin malaman da gwamnatin tarayya tun bayan da su ka shiga yajin aiki a ranar 4 Ga Nuwamba, 2018.
An dai shirya za a gudanar da taron ne da karfe 5 na yamma daidai.
Wakilan Kkungiyar Malaman Jami’o’i sun isa wurin tun kafin karfe 5 na yamma din, amma kuma babu wakilan gwamnatin tarayya ko daya a wurin.
Sai karfe 6 daidai ne Ministan Kwadago Ngige ya isa. Amma kuma Ministan Harkokin Ilmi, Adamu Adamu bai je ba har zuwa lokacin da malaman suka fusata suka fice daga zauren taron.
Discussion about this post