• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

MATSALAR TATTALIN ARZIKI: Gaskiya ta fito daga bakin Buhari, Daga Ashafa Murnai

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
December 15, 2018
in Ra'ayi
0
Buhari Osinbajo Next Level

Buhari Osinbajo Next Level

Ranar Juma’ar nan da ta shige ce Shugaba Muhammadu Buhari ya shaida wa daukacin gwamnonin Najeriya gaskiyar halin da tattalin arzikin Najeriya ke ciki, inda ya ce musu a gaskiya ya na cikin halin kaka-ni-ka-yi.

Buhari ya ce kafin a tayar da komadar da ta komadar da tattalin arzikin kasar nan, sai an yi da gaske, kuma su ma gwamnonin sai sun tashi tsaye wajen tsuke bakunan aljihun su.

Fitowar wannan furuci daga Buhari ta bai wa jama’a da dama mamaki. Akwai wadanda ke kallon cewa tuni Najeriya ta hau saitin zama kasaitacciyar kasa, kamar yadda milyoyin magoya bayan Buhari ke ta kururuwar cewa tattalin arzikin kasar nan ya dawo.

Sannan kuma akwai masu kallon cewa farfaganda ce kawai gwamnati da magoya bayan ta ke yi, da ita kan ta gwamnatin da masu yarda da abin da ta fada ke cewa tattalin arzikin kasar nan ya dawo.

Sai dai kuma furucin da Buhari ya yi wa gwamnoni, wanda Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya, kuma Gwamnan Jihar Zamfara, Abdulaziz Yari ya bayyana wa manema labarai a Fadar Shugaban Kasa, ya warware duk wata farfaganda da rufa-rufar da gwamnati da mukarraban ta ke yi wa ‘yan Najeriya cewa tattalin arzikin Najeriya ya bunkasa.

RANAR WANKA….

Dama idan banda Najeriya, a wace kasa ce za a same ka ka na sayen litar man fetur naira 87, washegari a maida maka ita naira 145, jibi kuma a ce maka tattalin arzikin kasa ya inganta, kuma kai har ka yarda?

In banda Najeriya, ta ya za a same ka ka na canjin dalar Amurka a kan naira N190 zuwa N200, a wayi gari dala daya ta koma N365, kuma shekara uku kenan, tunda ta hau ba ta sauko ba, sannan kuma a ce maka tattalin arzikin kasa ya inganta, kai kuma ka yarda?

Shin idan ba a Najeriya ba, wace kasa ce ka na biyan naira N850,000 kudin tafiya aikin Hajji, a wayi gari farashi ya koma N1,500,000, sannan kuma a ce maka rayuwar ka ta inganta, kai kuma ka yarda?

Ka kasa tashi daga garin ku zuwa wani gari daga karfe 8 na dare, a tafiyar da ba ta wuce kilomita 50 ba, sannan kuma ka ce an ci gaba. Wa zai yarda da kai?

Dama idan ba a Najeriya ba, wace kasa ce wadda gwamnonin ta ba su iya biyan albashi, sannan kuma a ce an samu ci gaba kai kuma ka yarda?

Wace kasa ce in ba Najeriya ba, za a rika karrama wadanda ake zargi kuru-kuru da gurgunta tattalin arzikin jihar su da wawurar dukiya da kashe-mu-raba, sannan kuma kai talaka a zo a ce maka an samu ci gaba, kai kuma ka yarda?

Wace kasa ce idan ba Najeriya ba, gwamnati haka kawai za ta shafa wa allo fenti ta rubuta masa sunan cewa ta kafa sabon kamfani, ku kuma ku yi tsalle ku na murnar kun ci gaba, kai ka ce ana murnar bukukuwan Sallah da Kirsimeti?

Wace kasa ce idan ba Najeriya ba, abin da ku ke saye daga kasashen ketare ya nunka farashin sa, sannan kuma a ce muku tattalin arziki ya inganta, ku kuma ku yarda?

Idan ba Najeriya ba, a wace kasa ce ko tsinken sakace ko dutsin goge kaushi za ta samar wa jama’ar ta, sai ta ciwo bashi, kuma a ce maka tattalin arziki ya inganta, kai kuma ka yarda?

Ta ya za a ce tattalin arziki ya inganta alhali babu wani abu guda daya sahihi da za a iya nunawa a ce an gina a wurare kamar Kano, cibiyar kasuwancin Arewa, wanda zai inganta tattalin arzikin yankin?

WA ZAI AMINCE?

Wa zai amince ya shigo Najeriya da dimbin dukiya ya zuba jari, alhali yankin jihohin da ya kamata a inganta sun shiga masifar garkuwa da mutane?

Ba ka iya barin Abuja ko Kano ko Kaduna ka tafi kauyen ku ka kwana, saboda ka na gudun kada masu garkuwa da mutane su ji labarin an yi bako mai sabuwar riga, su kuma su sungume ka. Sannan kuma an ce maka an samu ci gaba, kai kuma ka yarda. Shin karya ce wannan ko yaudara ko kuma rainin wayo?

Ta yaya wasu kamfanoni daga waje za su shigo su kafa masana’antu a lokacin da gwamnati ke cewa ta gama da Boko Haram, alhali ko makaho ya san ba a gama da su ba?

Ta yaya tattalinn arzikin masu karamin karfi zai inganta, alhali bashi ko lamunin kudin noman rani an rika saka siyasa ciki, ana bayar da shi har ga ‘yan siyasa maimakon wadanda ya kamata su rika cin moriyar sa?

Don me kuwa tattalin arziki ba zai shiga kaka-ni-ka-yi ba, tunda an kasa gane alkiblar da yaki da cin hanci ya sa a gaba? Saboda me aka kasa gurfanar da makusanta da na cikin gwamnati, wadanda ake zargi da wawurar bilyoyin kudade kafin su canja sheka?

Ta yaya wasu za su maida hankali su bazama su na gina masana’antu a jihohin da ake ci gaba da garkuwa da mutane, a gefe daya gwamnati ta fi maida hankali wajen tura ‘yan sanda 30,000 kula da zaben da masu kada kuri’a ba su kai milyan daya ba?

Ta yaya tattalin arziki zai inganta a jihohin da kowane gwamna sai dai ya mike kafa ya jira kason ribar man fetur a karshen wata daga Abuja?

Ta yaya rayuwar jama’a za ta inganta alhali asibitoci sai kara lalacewa da rashin likitoci su ke yi. Ta ya za a ce rayuwa ta inganta a gwamnatin da har yanzu sai maras lafiya ko majinyaci ya bi layin awa biyar kafin ya ga likitan da zai duba shi a cikin minti hudu?

Dama ya za a ce mana rayuwa ta inganta mu kuma mu yarda, tunda masu fita neman magani, ganin likita da binciken lafiyar jiki zuwa kasashen waje sai karuwa suke yi, maimakon raguwa?

Ba ka yi amanna da asibitocin Najeriya ba da tsarin ilmin Najeriya da titinan cikin jihohin Najeriya, duk ba ka mu’amala da su. Sannan kuma a bay aka ce ka ce mana Najeriya ta inganta, mu kuma mu yarda?

Ta yaya za a ce rayuwa ta inganta a lokacin da an fi maida hankali wajen sake cin zabe bisa ga magance manyan matsalolin da suka fi shafar talakawa gadan-gadan?

Ta ya za a yi kasashen duniya su dauke mu da muhimmanci, alhali ba mu bin umarnin kotu a kan hukuncin da bai yi daidai da abinda ran mu ke so ba?

Da wace hujja za a ce tattalin arziki ya inganta, alhali har yau masu mulki ba su gamsu da ilmin da suke bai wa ‘ya’yan talakawa ba? Ko kuwa sun fara maida ‘ya’yan su zuwa firamare da sakandare na gwamnati, kamar yadda suka yi alkawari kafin zaben 2015?

Wa ya taba jin masu mulki na kukan hujewar aljifan su? Saboda su dai ba su san tattalin arziki ya shiga taitaiyin sa ba. A karkara da kananan garuruwa nan ne a ke cin kwakwa. Amma yadda fadar shugaban kasa da gwamnoni da sanatoci da mambobin majalisar tarayya suka rika fantamawa a waccan gwamnatin, a yanzu ma haka su ke fantamawa.

Ita kanta siyasar ma da aka ce za a tsaftace, ko wankan-Gwari ba a yi mata ba, ballanatana a wanke ta da soso da sabulu. Shin ko shugabannin APC sun daina yawo da dimbin matasa dauke da makamai ne irin yadda suka rika tsine wa gwamnatin baya, har su na rantsuwar cewa idan sun hau za su kawar da wannan dabbancin?

Na dai yarda an samu ci gaba wajen yawaitar matasan mawaka masu farfagandar yekuwar tallata gwamnati, sai kuma dandazon sojojin baka ‘yan soshiyal midiya wadanda ba su ganin laifin wannan gwamnatin. Sai dare ya raba tsaka, ka gama wakar ka ko tura bayanai a soshiyal midiya, ka daga kai ka kalli sili, ka rasa tuna abinda aka yi wa al’ummar garin ku har rayuwar su ko tattalin arzikin su inganta.

Ka na nan ba da dadewa ba za ka ga wasu sun fito su na cewa Buhari bai ce tattalin arzikin Najeriya ya shiga halin kaka-ni-ka-yi a gwamnatin sa ba.

Mai karatu ka rubuta ka ajiye, wata rana sai ka ce ai kuwa dama na fada.

Tags: AbujaLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMEStallalin arzikiTattalin
Previous Post

Sojojin Najeriya sun fasa korar UNICEF daga Arewa maso Gabas

Next Post

Na kosa in gwabza da Buhari a Muhawara – Atiku

Next Post
Atiku-Buhari

Na kosa in gwabza da Buhari a Muhawara - Atiku

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Peter Obi ya fice daga PDP
  • Ba mu yadda mu janye wa mutum ɗaya ba, a shiga filin daga a fafata kawai – Ƴan takarar gwamnan Jigawa
  • AN YANKA TA TASHI: A biya ni naira miliyan 21 kuɗin fom ɗin takarar gwamna da na siya a PDP – Ɗan takarar gwamna
  • ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC
  • TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.