• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

2019: Yadda santsin siyasa ya kayar da ministocin Buhari

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
December 3, 2018
in Rahotanni
0
Buhari and Abebayo Shittu

Buhari and Abebayo Shittu

Fitowa neman takara ko shiga zaben fidda gwanin siyasa, tamkar cinikin biri ne ya na saman bishiya. Idan ba a tarba maka ka kama ba, ko kuma an samu wani baushi gwanin harbi ya rikito maka shi kasa ba, to biri bai zama na ka ba.

Shi kuwa Bahaushe da ya ke ya san fari da bakin siyasa, kuma ya san hairi da sharrin ta, sai ya ke mata kirari da: Siyasa romon jaba, ga kitse ga wari!

Daga cikin dubban ‘yan siyasar da suka fito takarar zabukan fidda gwani a jam’iyyun siyasa daban-daban, akwai ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari su shida.

Duk da cewa Buhari ya albarkaci takarar su da kuma nuna amincewa da su, hakan bai kais u ga nasarar fitowa wakilan jam’iyyar APC a zabukan 2019 mai zuwa ba.

Ko dai an nuna musu tuggun siyasa ko kuma an nuna musu cewa su kananan ‘yan jagaliya ne, wadanda tsoffin ‘yan alewa da sabbin yanka rake suka yi musu tadiya, santsin siyasa ko talalabiya ta kwashe su, ta rumtuna su da kasa.

Daga cikin ministocin Buhari shida, daya ne kawai ya sha da kyar, har ya samu takarar zaben 2019 a karkashin jam’iyyar APC.

KAYODE FAYEMI SHUKA GYADAR-DOGO

Ministan Harkokin Ma’adinai, Kayode Fayemi ne kadai wanda ya tsallake siradin santsin siyasa. Fayemi ya sauka daga minista, ya tsaya takarar zaben gwamnan jihar Ekiti, kuma ya yi nasara.

Dama a baya ya taba yin gwamna a Ekiti, amma Ayo Fayose ya kayar da shi a zaben gwamna, inda shi ma a lokacin Fayose din ya koma a karo na biyu a 2014.

A yanzu dai Fayemi gwamna na a karo na biyu. Shin kam siyasa ta yi masa gyadar-dogo, sama ‘ya’ya, kasa ma ‘ya’ya.

MAMA TARABA TA YI JIFAR-GAFIYAR-BAIDU

Aisha Alhassan, tsohuwar Ministar Harkokin Mata da Adebayo Shittu, Ministan Harkokin Sadarwa, ba su samu nasara a zaben fidda-gwanin jam’iyyar APC ba. Tun a wurin tantance sunayen ‘yan takara ne shugabannin jam’iyyar APC suka ki tantance su.

Ita Mama Taraba, takarar gwamnan jihar Taraba ta nema, kamar yadda ta fito a zaben 2014, a karkashin jam’iyyar APC, amma ba ta yi nasara ba.

Shi kuma Adebayo Shittu, ya so tsayawa takara ne ta gwamnan jihar Oyo.

APC ta soke takarar Mama Taraba saboda kusancin ta ga dan takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Tun a cikin 2017 Aisha ta fito ta nuna wa duniya cewa ita fa har yanzu ta na da muba’iya ga ubangidan siyasar ta, Atiku Abubakar.

Alhassan ta yi wannan kalami ne a lokacin da ta ke kan mukamin minista, a karkashi gwamnaatin Buhari.

Shi kuwa shugaban APC Adams Oshimhole, ya nuna cewa zai yi maganin ta, kuma shi ba shi da hakuri kamar Buhari.
Wancakali da APC ta yi a wurin tantance ‘yan takarar APC na gwamnan jihar Taraba, sai ta fice daga jam’iyyar ta koma UDP.

RAMUWAR GAYYAR MAMA TARABA A KAN APC

Ba ta dade da ficewa daga jam’iyyar APC ba, sai Mama Taraba ta kwashi motocin daukar kaya cike da karti, ta dumfari sakateriyar APC ta jihar Taraba, da ke Jalingo a fusace.

A cikin hasala ta sa aka kwashi duk wani abu mai amfani a cikin ofisoshin sakateriyar. An kwashi tebura, kujeru, firji, da duk wani abin amfani daga kayan bukatun aikin ofishin APC aka watsa cikin motocin da ta je da su. Ganau ba jiyau ba ya hatta labulaye ba ta bari ba, sai ta ta tsinke su, ta yi gaba da su.

Jummai, wadda aka fi sani da Mama Taraba, ta shaida wa manema labarai cewa duk it ace ta sayi kayayyakin da kudaden ta. Don haka a cewar ta, ba za ta raka asara da guda ba, tunda an hana ta takara, kuma ta fice daga jam’iyyar ba.

ADEBAYO SHITTU: BAKI SHI KE YANKA WUYA

Shi kuwa Minista Adebayo Shittu, shi da kan sa a baya a tabbatar da cewa bai je aikin Bautar Kasa ba, bayan da ya kammala dirigi din sa na farko.

Ya amince da haka ne bayan PREMIUM TIES ta fallasa cewa shi ma Shittu kamar tsohuwar minista Kemi Adeosun, bai je aikin bautar kasa ba, wato NYSC.

Fitowar labarin ke da wuya, sai ya ce tabbatas bai je aikin bautar kasa a shekarar 1979 da ya kammala kartun digiri din sa na jami’a ba.

Shittu ya kafa alilin cewa bai je bautar kasa ba, saboda a shekarar ne kuma ya shiga takarar zaben dan majalisar jihar Oyo kuma ya yi nasara.

A na sa tawilin, Shittu ya ce shi a zaton sa, wancan aiki da ya yi na dan majalisa duk ya shafe rashin zuwan sa aikin bautar kasa.

Sai da kuma shi shugaban APC, adams Oshimhole ya ce kowa ya san kin zuwa aikin bautar kasa, babban laifi ne, kuma akwai dokar da ta hana ma dauki ma’aikaci in dai har bai je aikin bautar kasa ba.

MUSTAPHA SHEHURI: SAKI RESHE KAMA GANYE

Ya na zaman sa a matsayin Karamin Ministan Ayyuka, Makamashi da Gidaje, ya ajiye mukamin sa ya shiga neman takarar gwamnan jihar Barno a karkashin APC.

Ganin cewa ya na Ministan Buhari, ya shiga takarar zaben fidda gwani a cikin zaratan masu takara 31.

Ana kusa da zaben fidda gwani sai masu takara 21 suka janye, suka bar wa Babagana Umara-Zullum.

Yayin da aka fafata takara tsakanin Zullum da sauran ‘yan takara goma da ba su janye ba, ciki har da Shehuri, Zullum ya samu kuri’u 4,432, shi kuma Shehuri guda 1 kacal. Wannan fa shi ne Hausawa ke cewa haihuwa daya horon tukiri.

Shehuri ya ji ciwon kayen da aka yi masa. Duk da cewa akwai wasu ‘yan takarar da suka samu kuri’u kudan 20, ba su korafi da raki kamar Shehuri ba.

Domin shi har manema labarai ya tara, ya bayyana ceea an yi magudi, rashin adalci da kuma fashin ‘yancin jama’a da rana tsakar rana.

Shehuri ya ji zafin kaye sosai, ya yi kuka, ya yi kururuwa, ya yi bobbotai. Kai irin yadda ya rika furta bakaken kalamai a gaban manema labarai, ba zai rasa yin Allah ya isa a zuciyar ba, idan har bai yi a sarari ba.

MANSUR DAN-ALI: NEMAN RUWA A HAMADA

Ministan Tsaro Mansir Dan-Ali ya nemi tsayawa takarar zaben gwamna a jihar Zamafara.

Tashin farko al’ummar jihar ba su yi na’am da shi ba, saboda duk da cewa ya na dan asalin jihar Zamfara, kuma ministan tsaro sunkutukum, bai tabuka abin kirki wajen mamayar da mahara, makasa kuma masu garkuwa da jama’a suka yi wa jihar Zamfara ba.

A farkon dawowar mulkin farar hura a 1999, Zamfara ta yi suna a duniya, saboda kaddamar da Shari’ar Musulunci da aka yi a jihar.

A yanzu kuma jihar Zamfara ta yi kaurin suna a duniya, saboda yadda masu samame suka mamaye jihar, ta yadda al’ummar jihar sun shiga cikin mawuyacin halin kisa, sata, fashi da garkuwa da mutane.

Rikicin zaben fidda gwanin da ya dabaibaye jihar Zamfara ya sa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC haramta wa jihar Zamfara zaben 2019.

UGURU USANI

Shi ne Ministan Kula da Harkokin Neja Delta. Buhari ya sa masa albarkar tafiya neman takarar gwamna a jihar Cross Rivers.

Sai dai kuma Uguru ya sha gurgura a hannun abokin takarar sa, Sanata John Owan-Enoh, wanda ya samu kuri’u 82, 227, shi kuma Uguru aka gurgura masa kuri’un hana-rantsuwa guda 1,437.

DA SAURAN RINA A KABA

Masu hangen nesan siyasa na ganin cewa wadannan ministoci da aka kayar a zaben fidda-gwani, ba za su zage damtse wajen ganin APC ta samu gagarimar nasara a jihar su ba, musamman a zabukan mukaman da aka kayar da su.

Wasu ma na ganin cewa hatta a zaben shugaban kasa ba za su yi gumi har su yarfe domin ganin Buhari ya yi tazarce ba. Domin sun san ko ma APC ta sake samun nasara, to da wuya a sake tafiya tare da su a matsayin ministoci, mukaman da suka raina har suka jaraba neman gwamna.

Tags: APCfashiHausaINECKisaLabaraiNajeriyaSataShittuZamfara
Previous Post

Har yau ba a kwaso gawarwakin ‘yan sandan da maharan Zamfara suka kashe ba

Next Post

Sakamakon kirgen yawan masu dauke da cutar Kanjamau a Najeriya zai fito a watan Maris – NACA

Next Post
Testing of Patience

Sakamakon kirgen yawan masu dauke da cutar Kanjamau a Najeriya zai fito a watan Maris - NACA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RANAR IYALAI TA DUNIYA: Ma’aikatar Jinƙai za ta agaza wa iyalai mabuƙata 30
  • Zan yi wa matsalar tsaro kifa ɗaya kwala ne idan aka zaɓe ni shugaban kasa – Amaechi
  • Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra
  • Tukunyar iskar gas ce ta fashe a kasuwar sabon gari dake Kano ba tashin bomb bane – Kwamishinan Dikko
  • Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.