Idan ba a manta ba rundunonin tsaron Najeriya da suka hada da na ‘yan sanda da Soji sun yi arangama da ‘Yan shi’a a garuruwan Zuba, Maraba da cikin garin Abuja a makonnin da suka gabata.
A wannan arangama dai an kashe ‘yan shia da dama sannan wasu da dama sun tsira da rauni a jikkunan su. Haka suma jami’an tsaro ba su sha da dadi ba daga hannun ‘yan shi’a domin sun ragargaza musu motoci sannan sun ji wa wasu jami’an tsaron rauni.
Bayan haka sun banka wa motar ‘yan sanda wuta inda suka yi amfani da bam din kwalba da ake hada wa da fetur. Sannan ‘yan sanda syn kama su da makamai da dama da ire-iren bama-bamai na fetur.
Zuwa yanzu an gurfanar da wadanda aka kama a wannan hargitsi.
Ga sunayen wadanda suka rasu kamar yadda aka fitar.
1. Abdulaziz Ibrahim (Maigana, Kaduna State)
2. Rabi’u Abdulwahab (Malumfashi, Katsina State)
3. Minka’ilu Shu’aibu (Kudan, Kaduna State)
4. Muhammad Hussain (Sokoto, Sokoto State)
5. Abdu Dijana (Suleja, Niger State)
6. Ukasha Dayyabu (Madalla, Niger State)
7. Faru’q Ahmad Garba
8. Sulaima SK
9. Muhammad Soje
10.) Fatima Yahaya Musa
11. Malam Abu Qasim (Gaji, Bauchi State)
12. Surajo Adam (Garu, Borno State)
13. Ja’afar Yusuf (Keffi, Nasarawa State)
14. Saeed Adamu (Awe, Nasarawa State)
15. Lawal Ibrahim (Tudun Baushe Maraban Kafanchan, Kaduna State)
16. Kamal Muhammad Haruna (Kaduna, Kaduna State)
17. Al-Kasim Minka’il
19. Huzaifa Musa
20. Abdulaziz Haruna (Bauchi, Bauchi State)
21. Muhammad Sani Awwal (Bauchi, Bauchi State)
22. Zangina Muhammad Garba (Bauchi, Bauchi State)
23. Isma’il Shu’aibu Alramma (Bauchi, Bauchi State)
24. Aliu Munnir (Mutum Biyu, Taraba State)
25. Hamisu Muhammad (Zaria, Kaduna State)
26. Abbas Muhammad
27. Munnir Muhammad (Samaru Zaria, Kaduna State)
28. Sa’id Zubairu (Maraba Abuja, FCT)
29. Abdullahi Sabo Muhammad (Yauri, Kebbi State)
30. Umar Abdullahi
31. Mansur Lawal (Bauchi, Bauchi State)
32. Umar Abdullahi Dogon Haris (Adamawa State)
33. Abubakar Dadda’u (Gombe, Gombe State)
34. Imrana Abdullahi.