Gwamnatin tarayya ta yi kira ga gwamnatocin jihohi da su dage wajen wayar da kan mutane game da hadarin dake tattare da kamuwa da zazzabin Lassa.
Bincike ya nuna cewa a watanni 11 da suka gabata mutane 559 sun kamu da cutar a inda 143 daga ciki suka riga mu gidan gaskiya.
A dalilin haka ne ministan kiwon lafiya Isaac Adewole ya bayyana cewa wannan karon gwamnati ta fara shirin ganin cutar bata yadu a kasa ba ta hanyar fara shiru tun yanzu da kuma wayar wa mutane kai game da cutar da yadda za su kiyaye kan su.
” A yanzu haka mun horas da m’aikatan da za su wayar wa mutane kai musamman a yankunan karkara.
” Asibitocin mu na ajiye da magungunan kawar da wannan cuta na zazzabin Lassa.
A karshe hukumar hana yaduwar cututtuka ta kasa (NCDC) ta bayyana cewa za ta hada hannu da kungiyar kiwon lafiya ta duniya (WHO) domin inganta ayyukan su game da cutar.
Discussion about this post