Shugaba Muhammadu Muhammadu Buhari ya amince da nadin wasu manyan mukamai biyar da kuma na wasu Manyan Daraktoci biyu na Hukumomin Gawamnatin Tarayya.
Cikin wadanda aka nada din har da surikin Buhari, mai suna Junaid Abdullahi, wanda aka bai wa shugabancin Babban Sakataren Hukumar Raya Yankunan Kan Iyakakokin Najeriya (BDCA).
An nada Junaid tun a ranar 22 Ga Satumba, kuma zai shafe shekaru hudu ya na shugabancin hukumar.
Ranar Juma’a ne Babban Sakataren Ayyukan Yau da Kullum na Ofishin Babban Sakataren Gwamnatin Tarayya, Olusegun Adekunle ne ya bayyana nade-naden na su a ranar Juma’a da ta gabata.
Kafin ranar Juma’a dai ba a sanar da cewa an nada surikin na Buhari a kan mukamin ba, an rufe batun, domin tun a ranar 22 Ga Satumba aka nada shi kan mukamin.
Discussion about this post