• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

AN YANKA TA TASHI: Dalilan Da Ka Iya Hana APC Shiga Zaben 2019 A Jihar Ribas

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
October 25, 2018
in Babban Labari, Rahotanni
0
Rotimi Amaechi

Rotimi Amaechi

Alamomi daga hukuncin da Kotun Koli ta yanke na nuni da cewa zai yi wuya APC ta shiga takarar Zaben Gwamna, na Majalisar Dattawa, Majalisar Tarayya har da na Majalisar Dokokin Jihar Ribas da ke karatowa a 2019.

Hukuncin da Kotun Koli ta yanke na soke zaben shugabannin jam’iyyar APC na jihar Ribas dungurugum, ya nuna cewa sauran ragowar karar da ke gaban Kotun Daukaka Kara ma dangane da zaben fidda gwani, zai kasance haramtacce ne.

Mummunan rikici a cikin jam’iyyar APC ta jihar Ribas ya kara ruruwa ne sakamakon adawar da ke tsakanin Ministan Harkokin Sufuri, Rotimi Ameachi da kuma Sanata Magnus Abe daga jihar.

Abe ya nemi tsayawa takarar gwamna, amma da ya ke jam’iyyar na a karkashin Ameachi, sai ministan ya kawo masa cikas din rashin amincewa.

TSAKANIN BIRI DA KAREN BAMAGUJE

Tun da farko matakin da Ameachi ya fara dauka, shi ne hana magoya bayan Abe shiga zaben shugabannin jam’iyya, da aka fi sani da ‘congress’. Ameachi ya kankane jam’iyya, sai abin da ya ga dama za a yi, kuma sai wanda ya ga dama zai ce a bi.

Shi kuwa Abe bai kwanta ya shantake ba, sai ya garzaya kotu, inda ya kalubalanci zaben shugabannin jam’iyya, a bisa dalilin cewa ba a bai wa magoya bayan sa damar shiga zaben ba.

A zaben shugabannin jam’iyyar dai an zabi dan gaban-goshin Amaechi, Ojukaye Amachree a matsayin shugaban jam’iyya na jiha.

Kwanki kadan kafin zaben sai Magnus Abe garzayawa Babbar Kotun a karkashin Mai Shari’a Chinwendu Nwogu, wanda shi kuma ya bayar da umarnin kada APC ta yi zaben shugabanni sai ta kammala hukuncin karar da Abe ya shigar.

Bangaren Ameachi ya daukaka kara, inda Kotun Daukaka Kara ta jingine hukuncin Babbar Kotu. Sai dai kuma Magnus Abe bai tsaya nan ba, ya garzaya Kotun Koli.

Kunnen-kashin da APC ta nuna na kin bin umarnin kotu har ta shirya zaben fidda-gwani a jihar Rivers a ranar 10 Ga Oktoba, hakan na nufin haramcin takarar dan gaban goshin Amaechi, Tonye Cole a matsayinndan takarar gwamna a jihar. A bisa dalilin cewa magoya bayan Magnus Abe nan ma ba su shiga zaben ba.

Haka kuma ya shafi zabukan fidda gwanin takarar sanatoci da na majalisar tarayya da na majalisar dokokin jihar.

Amma Kotun Daukaka Kara ba kai ga jaddada wannan hukuncin ba tukunna.

Abe ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa su Amaechi sun rika yin yadda suka ga dama, su ka ki bin umarnin kotu, suka gudanar da zaben shugabanninn jam’iyya da na fidda gwanin ‘yan takara, bayan kuma kotu ta ce kada a yi, tunda akwai shari’a da ake yi akan su.

A hukuncin da Kotun Koli ta yanke ranar Litinin da ta gabata, ta yi kaca-kaca da Kotun Daukaka Kara, a kan yadda ta soke umarnin da Babbar Kotu ta bayar.

“Wannan magana ce mai karfi sosai, kuma abin damuwa ganin yadda APC ta take dokar kotu, ta gudanar da abin da ta ga dama.” Haka Centus Nweze ya furta a madadin alkalan Kotun Koli biyar din da suka soke zaben shugabannin jam’iyyar APC na jihar Ribas.

RA’AYIN LAUYOYI A KAN HUKUNCIN DA AKA YI WA APC

Lauyoyi da dama da suka zanta da PREMIUMTIMES sun bayyana cewa hukuncin da Kotun Koli ta yi wa APC ya yi daidai, domin kiri-kiri ta take umarnin kotu.

“Bai ma kamata ba tun farko Kotun Daukaka Kara ta saurari karar da APC ta shigar a gaban ta ba, domin akwai umarnin dakatar da gudanar da zabe wanda ita APC din ta karya.” Inji lauya Malachy Ugwummadu, mazaunin Lagos.

Shi ma wani lauya mai suna Inibehe Effiong, cewa ya yi makomar wannan hukunci shi ne APC ba za ta iya tsaida ‘yan takarar gwamna, sanatoci, na majalisar tarayya da na majalisar dokoki ba a zaben 2019, a jihar Rivers.

Ya ce har sai an jira dayan hukuncin da wancan daukaka kara da ke gaban Kotun Daukaka Kara za ta yanke tukunna, wanda kuma zai iya haifar da daukaka kara zuwa Kotun Koli.

TAKARAR RIBAS: HANA WANI HANA KAI

Lauyan ya ci gaba da cewa a yanzu dai Magnus Abe na kwana da tashi a cikin murna, amma fa zai yi makukar wahala shi ma ya samu tikitin takarar ko da kuwa an soke Tonye Cole, dan takarar da Amaechi ya goya wa baya.

“Zai yi wahala, saboda Sashe na 87 na Dokar Zabe ya nuna cewa tilas sai an yi takarar fidda gwani dan takara zai iya fitowa. To tunda Kotun Koli da kan ta ta ce ba a yi zaben fidda gwani ba, kenan Abeh da Cole duk ba su shiga zaben fidda gwani ba kenan.” Inji shi.

Wani lauya mai suna Abdul Mohammed, cewa ya yi idan har Kotun Koli ba ta jingine hukuncin da Babbar Kotu ta yanke tun da farko ba, to babu yadda za a yi APC ta shiga zabuka a jihar Ribas.

Amma idan aka jingine hukuncin inji lauya Mahmood.

Ya ce amma idan aka jingine hukuncin, zai yiwu watakila APC ta fito da wasu ‘yan takara.

Sai dai kuma ya ce ganin yadda wuri ke kurewa, na wa’adin kwanakin da jam’iyya za ta iya sauya sunayen ‘yan takara, zai yi wahalar gaske APC ta tsaida ‘yan takara a jihar Ribas, muddin aka ci gaba da tafka shari’a.

MATSALAR AMAECHI A JIHAR RIBAS

Gwamnatin Jihar Ribas ta zargi tsohon gwamna Rotimi Amachi da salwantar da naira bilyan 112 wadanda ta ce ya tara bayan ya saida wasu kadarorin jihar a wani hamshakin attajiri, ana kusa ga yin zaben shugaban kasa na 2015.

Gwamanti karkashin sabon gwamna, Nyesom Wike na PDP sai ta nada kwamitin bincike, inda kwamitinn ya gano cewa dukkan kudaden da aka biya na kadarorin da Amaechi ya saida wa attajiri Tonye Cole, duk an karkatar da su.

Kwamitin bincike ya kuma zargi Amacchi da yin amfani da kudaden masu dama wajen daukar nauyin kamfen din Shugaba Muhammadu Buhari a zaben 2015.

Nyeson Wike gwamna mai ci a yanzu ya zargi Amaechi da cewa ya na tsoron a tuhume shi, shi ya sa ya rika garzayawa kotu, ya na nema kotu ta hana binkiken sa da gwamnatin Jihar River ta nemi a ji tun cikin 2015 da ya kammala wa’adin san a gwamna, wanda daga bisani ya zama ministan Buhari.

An yi zargin cewa Amaechi na ta kokarin ya boye gagarimar satar da ya yine a jihar Ribas shi ya sa ya tsaida attajiri Tonye Cole, wanda ya saida wa kadarorin a matsayin dan takarar gwamnan jihar Ribas a zaben 2019.

A yanzu dai batun tuhuma ko rashin tuhumar Amaechi na can makale a Kotun Koli, sama da shekara daya, ba a yanke hukunci ba.

Tags: AMaechiColeHausaLabaraiMagnusNajeriyaPREMIUM TIMESRibas
Previous Post

Oshiomhole dan jagaliya ne, bai cancanci shugabancin APC ba – Gwamna Akeredolu

Next Post

Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC

Next Post
Lanre Isa Onillu

Har yau ba mu da dan takarar gwamna a Jihar Imo –APC

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 11 da ake so a yawaita yi a watan Ramadan
  • ZABEN KADUNA: PDP ta yi murdiya a wasu kananan hukumomi, zan Kalubalance su a Kotu – Uba Sani
  • SABUWAR ƁARAKA A PDP: An dakatar da Fayose, Anyim, Gwamna Ortom zai gurfana gaban kwamitin ladabtarwa
  • Yunƙurin ‘yan majalisar APC uku masu so a halasta tu’ammali da tabar wiwi ya samu cikas
  • ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Keyamo ya roƙi SSS su kama Obi da Datti, saboda furucin cewa ‘zaɓen 2023 daidai ya ke da mulkin soja’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.