Tsohon shugaban hukumar EFCC Nuhu Ribadu ya bayyana cewa yana nan a cikin jerin ‘yan takarar fidda gwani na gwamnan jihar Adamawa da za a yi ranar Alhamis a garin Yola.
Salihu Banwo, shugaban kwamitin kamfen din Ribadu ne ya sanar da haka a hira da yayi da manema labarai a garin Yola.
” Dama can babban dalilin da ya sa Ribadu ya janye daga takarar fidda gwani shine ganin yadda wasu suka yi babakere a zaben sannan da kamar ba za a yi adalci a zaben ba.
” Amma tunda yanzu haka uwar jam’iyyar daga Abuja ta gyara tsarin zaben hankalin mu ya kwanta kuma mun tabbata za ayi adalci a zaben. Muna kuma sa ran mu ne za mu yi nasara.
Ribadu ya ce yana nan daram a takarar.
Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar Alhamis, ranar zaben fidda dan takarar gwamnan jihar Adamawa sannan ta canja shirin zabe daga na wakilai zuwa kato bayan Kato.
Discussion about this post