Dan takarar gwamnan jihar Osun na jam’iyyar SDP, Omisore ya bayyana cewa jam’iyyar APC zai yi a zaben da za ayi ranar Alhamis a jihar.
Idan ba a manta ba shine ya zo na uku a zaben da aka yi ranar Asabar a jihar da jam’iyyar PDP ta lashe zaben da bambamcin kuri’u 345.
Sai dai kuma hukumar zabe ta sanar cewa zaben bai kammalu bu ganin cewa kuri’un da aka soke sun fi yawan bambamcin da aka samu tsakanin APC da PDP.
Wadannan yankuna da za a yi zabe yankuna ne da Omisore yafi sauran ‘yan takarar sanuwa da tasiri wanda a dalilin haka APC da PDP suka fara zawarcin sa tun bayan sanar da cewa za a sake zabe a wadannan yankuna.
Omisore dai ya bayyana cewa zai mara wa jam’iyyar APC ce baya a zaben don samun nasara.
Discussion about this post