• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

An dora laifin ‘gargizar kasar’ Abuja kan gina rijiyon burtsatse barkatai

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
September 21, 2018
in Rahotanni
0
An dora laifin ‘gargizar kasar’ Abuja kan gina rijiyon burtsatse barkatai

Kwamitin da Shugaban Kasa ya kafa domin gano musabbabin jijjigar kasar da aka yi a Abuja, makonni biyu da suka gabata, ya dora laifin faruwar ta a kan yawan hakar rijiyoyin burtsatse barkatai da ake yi a garuruwan da ke gefen Abuja.

Mazauna yankunan Jabi, Gwarimpa da Mpape ne suka fi jin wannan jijjiga da kasa ta rika yi a kai akai har kwanaki biyu, Alhamis da Juma’a, 5 zuwa 7 Ga Satumba.

Duk da cewa ba wannan ne karo na farko da aka fara jin wannan jijjiga ba. Wannan da ta faru baya-bayan nan ta tayar da hankulan mutane sosai, kasancewa har cikin Abuja an rika jin jijjigar, musamman a a Maitama da kuma Garki.

Tun bayan faruwar lamarin dai Ministan Abuja Bello Mohammed ya hana gina rijiyoyin burtsatse, fasa duwatsu da sauran hakar ma’adinai a Abuja, musamman a yankin Mpape inda aka bayar da rahoton jijjigar ta fi karfi sosai.

Garin Mpape dai a kan tsauni ya ke, kuma kewaye ya ke da manya-manyan tsaunuka da suka kewayec Arewaci da Gabacin Abuja.

Bayan faruwar jijjigar, an kafa kwamitin bincike a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar Binciken Sararin Samaniya, Seidu Mohammed, wanda ya mika rahoton sa a yau Juma’a.

Sai dai kuma wasu mazauna yankunan sun nuna tsoro da kuma fargaba cewa jijjigar kasar da aka yi ta na da nasaba ne da yawan fasa duwatsu da ake yi a yankin Abuja, ba gina rijiyoyin burtsatse ba.

Kwamitin bincike ya tabbatar da cewa sun gano wasu wuraren da aka gina rijiyoyi na da nasaba da faruwar jijjigar kasar, wadda ta jijjiga hankulan mazauna Abuja da kewaye.

Yayin da kwamitin ke mika rahoton sa ga Ministan Kimiyya da Fasaha, Ogbonnaya Onu, ya bayar da shawar cewa gwamnati ta tsaurara matakan ayyukan da suka jibinci hakar duwatsu, rijiyoyin burtsatse da sauran ma’adinai a Abuja.

Daga nan sai kwamitin ya danganta jijjigar kasar da aka yi cewa ta faru ne sanadiyyar yadda a kullum ake kwalkwalar ruwa akalla metirik tan har 330,000 a Abuja da kewaye.

Kwamitin ya kara da cewa idan gwamnati ba ta yi hanzari ba, to irin wannan girgizar kasar za ta ci gaba da faruwa a Abuja, saboda yawan gina rijiyoyin burtsatse da ake yi barkatai.

Shugaban Kwamitin, Seidu Mohammed ya bayyana cewa akwai akalla rijiyoyin burtsatse 110,000 a Abuja da kewaye.

Rahoton ya nuna cewa yankin garin Mpape mai tsaunuka ne ya fi zama cikin barazanar yiwuwar girgizar kasa.

Haka nan kuma kwamitin ya tunatar da cewa wani rahoto da kamfanin Julius Berger ya bayar bayan ya gudanar da bincike, ya bayyana cewa yankin Mpape mai tsaunuka ba shi da karfin karkashin kasa sosai.

Tsandaurin karkashin kasar yankin ba shi da karfin rike jijiyoyin da suka rike farantin da ke tallabe da karkashin kasar baki daya.

Rahoton wanda Julius Berger ta fitar tun cikin 1978, ya nuna cewa yankin Mpape na daga cikin yankin da ake kira ‘Shear zone’ a duniya, wato inda ke fuskantar gafcewar girgizar kasa.

Idan ba a manta ba, bayann faruwar jijjigar kasar, gwamnati ta bayar da tabbacin cewa kowa ya kwantar da hankalin sa, jijjigar kasa ce, ba girgizar kasa ba.

PREMIUM TIMES a lokacin ta ruwaito cewa, Hukumar Agajin Gaggwa ta Babban Birnin Tarayya, Abuja, ta bayyana cewa babu alamomin yin girgizar kasa a cikin Abuja da kewaye, kamar yadda aka Ji kasa ta yi jijjiga wasu yankuna, musamman a Mpape da kewayen unguwannin gefen ta.

An dai ji wannan jijjigar kasa ne a ranar Laraba da dare zuwa Alhamis da safe, a Abuja, ciki kuwa har da yankin Gishiri Junction, NICON Junction da sauran wurare.

Wannan jijjiga dai ta razana mazauna yankunan sosai.

KADA A TAYAR DA HANKULA -Inji NEMA, kafin bincike

Sai dai kuma Daraktan hukumar NEMA, Abass Idris, ya ce ba abin tayar da hankula ba ne.

A wata hira da ya yi da NAN, a yau Juma’a, ya ce jijjigar kasar da aka ji a yankin Mpappe da wasu wuraren ciki har da Maitama, ba ya nufin akwai yiwuwar yin girgizar kasa a Abuja.

Ya ce wannan jijjiga ba ta rasa nasaba da wani irin karamin rugugin motsawar jijiyoyi ko igiyoyin da ke rike da kasa mai yiwuwa su tsinke yayin da motsawar ta wakana.

Wannan kuma inji shi, ba zai haifar da yiwuwar girgizar kasa ba.

“Lokacin da jami’an mu suka je wajen mazauna yankin Mpape, sun samu tabbacin cewa ba a wannan ne karon farko da hakan ta taba faruwa ba.

Sun ce an taba yin wannan jijjigar kasa shekaru biyar da suka gabata.”

Sai dai kuma ya ce akwai bukatar a duk lokacin da hakan ta faru, to mazauna yankin su gaggauta ficewa su sake wuri, kafin jijjigar ta lafa.

Ya roki mazauna yankin idan sun ji irin haka, to su shige a karkashin tebura su boye idan su na cikin daki ne.

Ya ce kuma a kauce daga jikin tagogi ko kyauren dakuna a lokacin da kasar ke jijjiga.

Sannan kuma kada a tsaya kusa da gine-ginen gidaje, ko karkashin manyan bishiyoyi da turakun wutar lantarki.

Wani mazaunin Maitama mai suna Victor Okoye, ya ce da ya ji rugugin kara ya dauka dutsi ne ake fasawa, amma sai ya ji wannan rugugin ya fi karfin fasa dutse.

“Ai da na fito daga gida sai na fahimci dai kasa ce ke jijjiga. Nan fa hankali na ya ba ni cewa, ai shikenan, tashin duniya ya zo.”

Wata mai suna Alice Adetola da ke Mpape kuwa, ta razana kwarai da gaske, ta ce haka su ma yaranta.

“Tashi na yi na rungume yara na, ina ta buga addu’a, domin na dauka ba za mu kai gobe ba.”

ALAMOMIN AFKUWAR GIRGIZAR KASA A ABUJA -Daraktan Gine-gine

Darakta Janar Danladi Matawal na Cibiyar Binciken Gine-gine da Titina, ya yi gargadin cewa kada fa Najeriya ta yi wa afkuwar jijjigar kasar da ta faru a Abuja rikon-sakainar-kashi.

Cikin wani bayani da ya fitar, ya ce tabbas akwai bukatar gwamnati ta gaggauta binciken musabbabin faruwar wannan jijjigar kasa a Babban Birnin Tarayya, Abuja, wadda ta afku a sassan Abuja a ranakun Alhamis da Juma’a.

Ya ce akwai bukatar Najeriya ta fito da tsarin da zai magance sake faruwar wannan jijjigar kasa, ya-Allah ko dalilin hakar kasa ne ta faru ko kuma a’a.

“In dai akwai inda aka rarake karkashin kasa ana gina titin karkashin kasa ko yin wani gini a karkashin kasa, to wannan gini kan iya kumbura jijiyoyin kasa har su fara jijjiga.” Inji Matawal.

“Su kan su mazauna Abuja na matukar bukatar da a horas da su matakan gaggawar da ya kamata su dauka a cikin hanzari, idan irin haka ta sake kasancewa.

“Idan wannan jijjiga kaddara ce daga Allah Ta’ala, to fa sai a yi shirin fara kwashe mutane daga Abuja ana ficewa, domin ita babbar girgizar kasa fa ta kan fara ne da ‘yar jijjigar kasa, dalili, saboda karkatsewa da daddatsewar da igiyoyi ko jijiyoyin karkashin kasa ke yi ko kuma saiwa-saiwar da ke rike da farantin da ke tallabe da jijiyoyin karkashin kasar su kan su.” Gargadin Matawal kenan.

“Wato aman wutar duwatsu da girgizar kasa duk wani balbalin bala’i ne wadanda Najeriya ba ta ma taba tunanin yi musu shirin ko-ta-kwana ba. To saboda ba a taba shirya musu din nan ba, sai jikin mu ke ba mu cewa kamar ba mu ma san da su ba, ko kuma ba mu yarda za su iya faruwa a nan ba.”

“Zan ja hankalin mu da cewa wani ya ba mu labari cewa a inda ya ke a garin Mpape, inda jijjigar kasar ta fi karfi, kare ya fara ji ya na ta haushi ba kakkautawa. Jin haka sai mu ka yi ta rafka addu’a cewa Allah dai ya sa wannan abu ba wani ibtila’i ba ne daga Allah.

“Domin idan ibtila’in girgizar kasa ce, to gargadin farko da jama’a za su fara ji shi ne dabbobi su fara firgita su na haushi, su na fafarniya.

“Za a ga karnuka sun kaure da haushi ba kakkautawa, maguna su kasa zaune, su kasa tsaye wuri daya, su na ta sagarabtu, beraye su rika gig-gilmawa cikin gida ko cikin dakuna a guje, kuma a rude. Dawaki kuma su rika harbin iska da haniniya su na fizge-fizgen tsinkewa daga turakun su, su na fagamniya a rude.”

“Ba wani abu ba ne zai sa su rika yin wannan sai saboda maganadison ji da sauraren su ya sinsino kuma ya fizgo musu karkarwar da karkashin kasa ke fara yi a lokacin da jijiyoyin karkashin kasa ke daddatsewa daga jikin farantin da ke tallabe da karkashin kasar baki daya.”

Ya ce mataki mafi sauki da kuma saurin dauka idan irin haka ta faru, to a yi gaggawar ficewa daga inda ake, a kwashi yara da kananan dabbobin da za a iya runguma, a runtuma a guje zuwa cikin fili ko sararin da babu gine-gine kusa.

Matawal ya ci gaba da bayar da wasu misalai da alamomin matakai har guda hudu masu nuni da cewa idan hakan ta auku, ko kuma ta fara aukuwa, to babu makawa girgizar kasa na tafe.

Tags: AbujaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Babban Bankin Najeriya CBN ta soke lasisin Bankin Skye

Next Post

Hukumar raba zakka na jihar Sokoto ta bada tallafin Naira miliyan 7.4 don gajiyayyu a jihar

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Jihar Sokoto ta kaddamar da shirin daukar dalibai

Hukumar raba zakka na jihar Sokoto ta bada tallafin Naira miliyan 7.4 don gajiyayyu a jihar

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kada ku tausaya min don na faɗi zaɓen Sanatan Zamfara – Sanata Marafa
  • JIRAN TSAMMANI: Tinubu zai saka wa waɗanda su ka yi wa APC hidima da waɗanda su ka wahala saboda jam’iyya – Marafa
  • Uba Sani ya yi sabbin nade-nade 27, ya nada Sani Liman shugaban ma’aikatan fadar gwamnati
  • SHUGABANCIN MAJALISAR DATTAWA: ‘A saka min wahalar da na yi wa APC, a ba ni shugabancin Majalisar Dattawa’ – Osita Izunaso
  • SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ba zan janye wa kowa ba, amma na ‘jone’ da guruf ɗin Abdul’aziz Yari’ – Orji Kalu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.