Mahara sun far wa wani gidan kallon kwallo dake Badarawa a karamar hukumar Shinkafi jihar Zamfara.
Maharan dauke da bindigogi sun kashe mutane 11 sannan wasu 21 sun tsira da raunuka a jikin su a daidai suna kallon kwallon a gidan.
Kakakin gwamnan jihar Ibrahim Dosara ya bayyana haka wa PREMIUM TIMES inda ya kara da cewa maharan sun far wa wannan gidan kallo ne a daren Laraba.
” A yanzu dai mutanen da suka sami rauni na samun kula a babban asibitin Shinkafi sannan jami’an tsaro sun fara gudanar da bincike domin gano wadanda suka aikata wannan mummunar aiki.
Sai dai kuma a jawabin da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Mohammed Shehu yayi, ya ce mutane shida ne suka rasa rayukan su a harin sannan 10 ne kawai suka sami rauni.
Shehu yace sun gaggauta zuwa wannan wurin ne bayan sanar dasu abin da ya faru a kauyen Badarawa.
Za mu bincika dazukan dake kewaye da kauyen Badarawa domin ta nan ne maharan suka gudu sannan za kuma mu kafa shingaye hanyoyin da ake shiga dajin.
Discussion about this post