Idan ba a manta ministan harkokin kudi na Najeriya Kemi Adeosun ta buga satifiket din karya cewa an yafe mata yin bautar kasa NYSC a Najeriya bayan ta kammala Jami’a.
Wannan karya da ta lafta ya tada hankulan mutanen Najeriya matuka ganin cewa gwamnatin da take wa aiki gwamnati ce da ke bugun kirji da yin kururuwar ita gwamnati ce mai tsafta.
Tabbatattu kuma sahihan shaidun bayanai rubutattu sun tabbatar da cewa Ministar Harkokinn Kudi, Kemi Adeosun ba ta yi aikin bautar kasa ba, kuma a lokacin shekarun ta ba su kai na wadda aka dauke wa aikin bautar kasar ba.
PREMIUM TIMES ta gano cewa Kemi ta mallaki shaidar yin bautar kasa ne ta hanyar yin fojare, shekaru da yawa bayan da ta kammala jami’a.
Yan Najeriya sun harzuka sosai bayan fallasa harkallar da Ministar Harkokin Kudade, Kemi Adeosun ta yi, inda ya tabbatar da cewa kiri-kiri ta ki zuwa aikin bautarc kasa wato NYSC, a lokacin da ta kammala babbar kwalejin ta.
Akasarin wadanda suka tofa albarkacin bakin su, sun yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya kafa kwamitin bincike domin a tabbatar da gaskiya ko akasin gaskiyar wannan labara da PREMIUM TIMES ce ta bankado shi.
Mafi yawan wadanda suka yi rubuce-rubuce a soshiyal midiya, sun cika da mamakin yadda hukumomi da jami’an tsaron bincikenn kwakwaf suka kasa gano wannan bahallatsa ta Kemi, har sai da PREMIUM TIMES ta fallasa ta.
Takardun karatun Kemi da ke hannun PREMIUM TIMES sun nuna cewa an ba ta satifiket na yafe mata zuwa bautar kasa a shekarar 2009, a bisa yawan shekaru.
Amma sai dai ko uffan har yanzu gwamnatin Buhari bata ce ba game da haka.
Sai gashi kuma gwamnatin kiri-kiri ta daure wani ma’aikacin ta wai shima ya aikata irin haka.
Kotu ta daure wani ma’aikacin ma’aikatar Kudi ta tarayya mai suna James Lebi-Ayodele da ta kama da laifin buga satifiket din karya na kammala karatun samun kwarewa a harkar kudi.
Bayan haka James zai biya taran Naira 100,000.
Alkalin kotun Yusuf Halilu ya bayyana cewa yanke wa James irin wannan hukunci zai zama darasi ga duk masu buga satifiket din karya.
Sai dai kuma ita ministan kudi, Kemi Adeosun, da yake shafaffa da mai ce, sannan tana da uwa a gindin murhu, gwamnatin Najeriya ta kasa ce mata ko kala, duk da ta yi amfani da shaidar karya ta dare kujerun iko da dama a kasar nan kuma an samu tabbacin lallai satifiket din bogi ne ta yi ta amfani da har ta kai matsayin da take yanzu a kasar nan.
Discussion about this post