• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TATTAUNAWA: Yadda rikici ya shiga tsakani na da Buhari -Gwamna Ortom

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 27, 2018
in Rahotanni
0
Samuel Ortom

Samuel Ortom

A doguwar tattaunawa da Gwamnan Jihar Benuwai Samuel Ortom ya yi da PREMIUM TIMES, ta bayyana dalla-dallar asalin rikicin sa da Shugaba Muhammadu Buhari da kuma rigingimun da ake samu a yankin Arewa ta tsakiya, wadanda ya ce ba rikicin makiyaya da manoma kadai ba ne ya dabaibaye yankin.

PT: Mun fahimci jirgin siyasar jihar ka ya na tangal-tangal cikin ‘yan kwanakin nan. Me ke faruwa ne?

Samuel Ortom: To, abin takaici ne kwarai, domin abin da ke faruwa a nan, da wata kasa ce mai wayewa da kuma ci gaba, to hakan ba zai faru ba. Amma nan a Najeriya, abin kamar ya ma zama kalubale a gare mu. Idan ka jajirce a kan gaskiya, adalci da bin ka’ida, to ka zama abin kalubalanta ga jama’a da yawa. Wannan shi ne abin da ke faruwa a jihar Benuwai.

Gaba dayan sabanin ya taso ne daga tsayawar da na yi ina neman kare hakkin al’ummar jiha ta. Amma ni ba ni da wata aniyar yin rigima da masu mulkin kasar nan, ko wani mutum shi daya tilo.

Ni dai na hau mulki cikin 2015, amma fadan da ake kira na makiyaya da manoma, ya dade ba tun yau ba. Daga 2011 a misali, ai ana wannan fadace-fadacen.

To mu sai muka zauna muka yi nazarin cewa, tunda dai an ce fada ne a tsakanin makiyaya da manoma, don me a kasashe kamar su Afrika ta Kudu, Switzerland da irin su Kenya duk ba a samun irin barkewar wannan rikicin? Ai a fadin duniya ana noma, kuma akwai makiyaya, amma ba a samun barkewar kashe-kashe da lalata dukiyoyi, sai nan a Najeriya.

Daga nan sai muka ga hanya mafita ita ce kamar yadda sauran kasashe suka yi, kuma suka zauna lafiya, wato a killace dabbobi kawai. Dalili kenan muka shigo da wannan doka ta hana kiwo barkatai a jihar Benuwai.

Kuma kafin a kafa dokar sai da aka kasa jihar Benuwai zuwa shiyya hudu inda aka wayar wa jama’a kai, kuma akasarin al’umma suka yi murna da wannan doka.

PT: amma duk da haka sai da Miyetti Allah ta yi kuka da wannan doka. Me ya sa?

Ortom: cewa suka yi ma ba zai yiwu a kafa wannan dokar ba. Wai su na da ‘yancin da za su rika yawon kiwo da dabbobin su inda suke ga dama, kuma ba wanda ya isa ya dakatar da su.

PT: Ashe kai ka shigo da batun dokar killace dabbobin kenan?

Ortom: E mana. Ai batun killace dabbobi wuri daya shi ne, ka tsare shabun ka wuri daya, ka tanadar musu da abincin su, har da ruwan shan su, don kada su afka cikin gonar wani ko wasu su rika yi musu barna.

PT: Ka ce rikicin ba na makiyaya da manoma kadai ba ne. Har da na me kuma?

Ortom: Kwarai kuwa, ai a kan hanyar yin wannan bayanin na ke. Mun sa wa dokar hana kiwo barkatai hannu a ranar 22 Ga Mayu, 2017, to a cikin watan Yuni, sai Miyetti Allah ta fito ta ce wannan dokar ba mai dorewa ba ce, karkon-kifi za ta yi, domin ba za su amince da ita ba. Kai har ma cewa kungiyar ta yi za ta tarkato kan mambobin ta domin su bijire wa dokar.

Ganin haka sai nan da nan na rubuta wasika zuwa Fadar Shugaban Kasa, kuma bayan na aika da wasikar sai na bi sayu da kai na domin zuwa ziyara fadar. Na rubuta wa jami’an tsaro cewa wadannan mutanen fa su na barazana. Kuma ni dama a iyar sanin da na yi musu, idan har shugabannin kungiyar Miyetti Allah ta furta wata barazana, to shikenan magana ta kare. Ni kuma sai na nemi jami’an tsaro su kama wadanda suka yi wannan barazana.

To cikin wannan shekara kuma sai wata kungiyar Fulani mai suna FUNAM ta kira taron manema labarai, ta ce za ta kaddamar mana. Ganin haka, sai na samu kwafen kalaman na su, na hada. Wasun su ma cewa suka yi ai batun na mamaye wannan yanki ne, domin wai a cewar su, yankin Benuwai din nan da muke ciki wai mallakin su ne.

PT: Ko ka samu zaunawa tare da shugaban kasa a kan wannan batun?

Ortom: Mun zauna, kuma na fada masa kukan mu, amma babu abin da aka yi, har sai cikin watan Janairu din nan, bayan mun kaddamar da dokar hana kiwo a ranar 1 Ga Nuwamba, 2017.

Wato idan ka lura mun bada rata domin kara samun maslaha, domin a cikin Mayu aka sa dokar amma ba a fara amfani da it aba, sai cikin watan Nuwamba. Muka ce matsawar makiyayi zai killace shanun sa a wuri daya, za mu zauna da shi babu wata tsangwamar juna, sai zaman lumana. Amma wanda duk ya ke ganin cewa shi ba zai iya killace shanun sa wuri daya ba, to sai ya tafi wata jihar ya nemi wani dajin da zai rika yawon kiwo da shanun sa a can.

Me zai faru, sai kawai muka wayi gari a ranar 1 Janairu, 2018, makiyaya suka kai wa jama’a mummunan farmaki, suka rika kashe jama’a har da kona kananan yara. Banda ma harbi da suka rika yi, sun kuma rika harbin jama’a da kibau, bayan sun kashe mutane kuma har daddatsa su suka rika yi.

An kawo jami’ann tsaro har da sojoji, amma kamen da aka yi bai taka kara ya karya ba. Su kuma sojoji sai ma suka rika raba takardun kiraye kirayen jama’a a zauna lafiya tsakanin makiyaya da manoma. Dalili kenan fadan a lokacin ya ki tsaywa.

Da shugaban kasa ya kawo ziyarar ta’aziyya, mun shaida masa cewa mun yi murna da kawo sojoji, amma aikin da suke yi, tamkar aikin-Baban-giwa ne. Kai, mu dai ba mu samu sauki daga kisan da mahara ke yi ba, har sai da aka kawo sojojin Operation Wild Stroke tukunna. Amma na Exercse Cat Race babu wani abin a zo a gani da suka tsinana mana.

PT: To amma ai su sojojin Operation Cat Race akwai lokacin da suka ce sun kama wani mai b aka shawara a fannin tsaro, da suka ce sun kama shi da laifin daukar nauyin masu kashe mutane.

Ortom: Ai ka ji irin ta. Maganar duk ta bata wa mutum suna ne domin a samu dalilin hukunta shi kawai. Ni dai babu ruwa na da daukar nauyin wasu kartin kauye masu kashe mutane. Kowa ya san ni, kuma duk jihar nan an san ni ko wane ne.

Saboda ma farkon abin da na fara yi da na hau mulki shi ne raba makamai daga hannun masu tayar da husuma a cikin 2015.

Har sharri ma sai da kala min wai ina daukar nauyin wasu makasa mutane su 600, kowane kuma ya na da bindiga samfurin AK47.

PT: Batun Tishaku

Ortom: Ina zuwa a kan sa dama. Ba ni na dauke shi aiki ba. Na tarad da shi ne gwamnatin da na gada ce ta dauke shi aiki a karkashin gwamnatin jihar Benuwai. Kuma tsohon Sufeto Janar na ‘Yan sandan Najeriya ne ya kawo shi domin ya rika shiga tsakanin makiyaya da kuma ‘yan asalin jiha don kada kashe-kashe su rika barkewa. An ce tubabben dan Boko Haram ne. kuma ba shi kadai ba ne na gada daga waccan gwamnatin, akwai matasa masu irin wannan aiki na Tishaku.

Ko lokacin da Buhari ya kawo ziyara, ai sai da Tishaku ya mike a gaban shugaban kasa din ya zayyana masa yadda aka yi ya zama dan Boko Haram, amma daga baya ya tuba. Ya ce masa mai bada shawara ga shugaba kan tsaro ne ma ya ceto shi lokacin da aka nemi kulla masa wani sharri. Ya kuma fada wa Buhari dai cewa Mataimakin Fufeto Janar na ‘Yan sanda da kan aiki ne a yanzu ya turo shi jihar Benuwai. An kwao kafin na zama gwamna fa.

Don haka ashe ma kowa ya san shi kenan a kasar nan, tun ma kafin na hau mulkin jihar Benuwai.

PT: Ba za mu manta ba, akwai lokacin da fadar shugaban kasa ta ce dokar da ka sa ce ta harzuka kashe-kashen da ya faru a jihar Bneuwai.

Ortom: To, idan har ka ji ministan harkokin cikin gida na irin wannan kalamin, idan kuma ka ji ministan tsaro na irin wannan kalamin dai, ko babban hafsan sojojin kasa, to wannan ya ishe ka hujjar sanin dalilin da ya sa na ke a cikin tsaka-mai-wuya.

Amma bari na tambaye ka, idan har an ce dokar da aka kafa ce dalilin kashe-kashen jihar Benuwai, to jihar Zamfara da Filato da Kaduna fa? Maganar dai ita ce waccan kungiyar Fulani da ta yi kasassabar kin bin doka, kai, ta ce ba ma magabar killace dabbobi ba ce, maganar mamaye yankin ce kawai. Zancen gaskiya kenan.

Tags: AbujaHausaLabaraiOrtomPREMIUM TIMES
Previous Post

KASAFIN KUDIN ZABE: Majalisa ta amince wa Hukumar Zabe Naira biliyan 143

Next Post

ZARGIN NEMAN MAZA: ’Yan sanda sun damke matasa maza 57 a cikin wani otel

Next Post
Police Force

ZARGIN NEMAN MAZA: ’Yan sanda sun damke matasa maza 57 a cikin wani otel

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Peter Obi ya fice daga PDP
  • Ba mu yadda mu janye wa mutum ɗaya ba, a shiga filin daga a fafata kawai – Ƴan takarar gwamnan Jigawa
  • AN YANKA TA TASHI: A biya ni naira miliyan 21 kuɗin fom ɗin takarar gwamna da na siya a PDP – Ɗan takarar gwamna
  • ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC
  • TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.