Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki ya sanar da ficewar sa daga jam’iyyar APC.
Saraki ya bayyana haka ne a shafin sa na tiwita, ya na mai cewa ya dauki wannan shawara ne bayan zurfin tunani da ganawa da yayi da makusantar sa da abokanan siyasar sa.
Shima gwamnan jihar Kwara, Abdulfatah Ahmed ya aanar da ficewa daga jam’iyyar APC din.