Shugaban hukumar bada agajin gaggawa na jihar Yola Musa Jidawa ya bayyana cewa ambaliyar ruwa ya rusa gidaje da dukiyoyin mutane da dama a yakin Damaturu.
Ya fadi haka ne ranar Laraba a ziyarar da ya kai yankunan da ambaliyar yayi wa ta’adi.
Bayan ziyarar wadannan unguwanni da suka yi, Jidawa ya ce gwamnati za ta ci gaba da agaza wa mutanen da suka rasa dukiyoyin su sannan za a kara wayar da kan mutane game da hadarin da ke tattare da zama a irin wuraren da suka yi gaba da kogi ko rafi.