Tun bayan kafa sabuwar jam’iyyar R-APC daga APC, zuwa yanzu siyasa ta dau zafin da banda yarfe gumi a goshi ba abin da jam’iyya mai mulki ke yi.
Shugaban APC Adams Oshimhole ya fita rangadin tausar kirgin manyan ‘yan jam’iyyar da suka fidda maitar ficewa jam’iyyar gaba daya.
Duk da haka, PREMIUM TIMES ta tsakuro wasu sanatoci 20 da ake kyakkyawan zaton ficewar su daga jam’iyyar.
Duk da dai ba laifi daya gaba dayan su aka yi musu ba, amma dai dalilan ba su wuce rikicin cikin jam’iyyar ne.
Akwai masu kulafucin shi kansa Shugaba Buhari da kuma dalilai na maida su saniyar-saniyar ware a jihihin su, musamman ga masu rashin jituwa su da gwamnonin jihar su.
1. Bukola Saraki
2. Dino Melaye
3. Shehu Sani
4. Suleiman Hunkuyi
5. Kabir Marafa
6. Sabi Abdullah
7. Rabiu Kwankwaso
8. Shaaba Lafiagi
9. Abu Kyari
10. Adamu Aleiro
11. Danjuma Goje
12. Isa Misau
13. Ibrahim Gobir
14.John Enoh
15. Ibrahim Danbaba
16. Suleiman Nazifi
17. David Umaru
18. Barnabas Gemade
19. Rufai Ibrahim
20. Bala Na’Allah
21. Mohammed Shittu