An dai yi an gama kuma an fadi sakamakon zabe, sai dai masu yin fashin baki a harkar zabe sun yi fashin bakin kan yadda kuri’u 19,338 ta ba da PDP a zaben Ekiti da aka yi a ranar Asabar.
Dan takarar gwamnan jihar a inuwar Jam’iyyar APC, Kayode Fayemi ne ya lashe zaben in da ya doke Ekele na jam’iyyar PDP, wato shafaffe da man tsohon gwamna, Ayo Fayose da kuri’u 19,338 kacal.
Abin da kamar wuya sai dai kuma mai aukuwa ta auku domin tuni hukumar zabe har ta bayyana Fayemi a matsayin sabon gwamnan jihar Ekiti.

Discussion about this post