Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa hadin kan kasar nan ba abin yin wasa ko yi masa rikon-sakainar-kashi ba ne, balle har wani ya shigo da son ran sa ya nemi sai an yi masa abin da ya ke so idan ana so a ci gaba da tafiya tare.
Daga nan sai ya ja hankalin kafafen yada labarai su guji yada abubbuwan da ka iya haddasa mummunan rikici a kasar nan.
Obasanjo ya yi wannan bayani a ranar Asabar yayin da ya zama mai masaukin baki a bikin shekara na Hukumar Gudanarwar Editocin Tsare-tsaren kamfanin Penpushing Media.
An gudanar da taron a Babban Dakin Taro na Laburaren Obasanjo da ke Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.
Ya ce sai ‘yan Najeriya sun riki kowane bangare na kasar nan a matsayin abokan gudu tare da tsira tare, sannan kasar nan za ta iya ci gaban da za a yi tinkaho da ita.
Ya ce bambancin kabilu da yaruka da addini wata albarka ce ga kasar nan, ba matsala ba ce.
Daga nan sai ya nuna takaicin sa matuka gaya a kan yadda jama’a da dama suka fara dawowa daga rakiyar gaskata kafafen yada labarai sosai.
Daga cikin manyan bakin da suka shugabanci zaman tattaunawar har mawallafin PREMIUM TIMES, Dapo Olorumi.
Discussion about this post