Hukumar kula da da jami’o’i na kasa ta mika wa sabuwar jami’a mai zamankanta ta farko a Jihar Kano.
Jami’ar mai suna Skyline University ta karbi shaidar amincewa ta fara aiki ne daga hukuma NUC ayu a Abuja.
Cikin Jami’o’i 75 masu zaman kan su dake kasar nan, kwaya biyu ne tal ke yankin Arewa Maso Yamma, da ya hada da Kaduna, Kano, Katsina, Sokoto, Kebbi, Zamfara, da Jigawa.
Al-Qalam dake Katsina da yanzu Skyline da za a bude a Kano mallakin Kamal Puri, wani dan kasar India.

Da yake mika shaidar amincewar ga shugaban Jami’ar Kamal Puri, dan kasar India, shugaban hukumar NUC Abubakar Rasheed ya ce jami’ar Skyline iat ce jami’a mai zaman ka an 75 da aka amince da a kasa Najeriya zuwa yanzu.
” Yanzu haka akwai jami’o’i mallakar gwamnatin tarayya 42 a kasar nan sannan akwai 47 kuma mallakar gwamnatocin jihohi da 75 yanzu dake masu zaman kansu.