Kasar Morocco ce kasa ta biyu da ga nahiyar Afrika da ta kwashi kashin ta a wasan kwallon kafa na cin kofin duniya da ake ya a kasar Rasha.
Kasar Urugay ta doke kasar Masar da ci daya mai ban haushi, haka da yamman Juma’ar yau, ita ma kasar Morocco ta kwashi na ta a hannu bayan mai tsaron bayan ta ya saka wa gidan sa kwallo a gaban tashi.
An tashi wasa, Iran 1 Morocco 0.
Gobe ne dai Najeriya za ta buga wasan ta na farko da kasar Crotia.