Kotun gwamnatin tarayya dake garin Kaduna ta bada belin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Ramalan Yero.
An gurfanar da Ramalan Yero a kotu ne bayan tuhmar sa da ake yi da waske wa da naira miliyan 700 kudin kamfen a 2015.
Jama’a masoyar sa sun yi tururuwa zuwa kotun dake Kawo domin yin zanga-zangar nuna fushin su ga daure Yero da akayi na kwanaki biyar.
A karshe, Kotu ta bada belin sa da sauran wadanda a ke tuhuma kan naira miliya dari.
Discussion about this post