• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Malamai da Shugabanni; Wanene matsalar Al’umma? – Daga Magajin Malam

Mohammed LerebyMohammed Lere
June 3, 2018
in Ra'ayi
0
Buhari and Bala Lau

Buhari and Bala Lau

Rashin cikkaken fahimtar Addini shine babban matsalar Al-Ummar mu amma har yanzu ba mu gane ba ballantana mu zurfafa ilimin Addini.

Za ka ji mutane su na cewa: idan aibanta shugaba bai halatta ba, to aibanta Malami ya halatta ne?

Wannan tambayar kawai ta tabbtar da karancin fahimtar Addininsu a fili.

Abunda ba su sani ba shine:

#Mugun Shugaba kokoluwar abunda zai bata maka shine jin dadin rayuwarka ta duniya. Kuma duk lalacewarsa yafi ace babu shi kwata-kwata, domin idan babu shugaba zaman gidanka ma ba zai yiwu maka ba ballanta fita waje, saboda kowa zai zama hukuma: mai karfi ya danne mara karfi, masu yawa su danne marasa yawa, mai kudi ya danne mara kudi, dss.

Da wannan ne Shari’a ta wajabta ma mabiya yin biyayya ga shugaba saboda an wakilta umurni da hani a hannunsa.

Saboda haka ne ma Manzon Allah (SAW) ya yi ma Sahabansa wasici da yin biyayya ga shugaba ko da kuwa bakin bawa ne Dan Habasha aka shugabantar da shi akansu, wannan misali ne na karfafa mahimmanci biyaya ga shugaba, lura da yadda Larabawa a jahiliya suke kyaman bakin mutum ballanta kuma ace bawa ne.

Sahabai (RA) ba’a taba samun dayan su da aibanta shugaba ba ballanta yi masa bore ko tawaye, duk da cewa mafi yawan su sun ga zamanin shugabanni daban-daban: Abubakar, Umar, Uthman, Ali, da Mu’awiyah (RA) dss. Tsakaninsu da shugabanni sai biyayya da Addu’ar Allah ya datar da su da abunda Yake so kuma Ya yarda da shi, domin jarabawa ce Allah Ya kaddara musu na yin shugabanci, wanda yi musu fatan alheri da dacewa da cin jaraba yana daya daga cikin hakkokinsu akan yan uwansu Musulmai. Yi musu bore da mugunyar Addu’a saba ma Allah ne da Manzonsa (SAW) da toye hakkin yan uwantaka na Musulunci wanda suke kawo fitintinu a cikin Al-Ummah.

Daya daga cikin magabata nagari yace: Da Allah zai yi masa alkawarin amsa masa Addu’arsa guda daya tak, to da zai yi ma shugaba ne ita na nema masa shiriyar Allah, domin idan ya shiryu Al-Ummah za ta shiryu.”

#Shi ko mugun Malami mugun makami ne wanda zai bata maka duniyarka da Lahira. Kamar yadda Manzon Allah ya fadi: “mugun Malami yana yin muguwar fatawa, ya bata ya batar…” Domin gama-garin mutum za su daukeshi a matsayin hujja na Addini. Idan Malami ya bi Allah da Manzonsa (SAW) ya kubuta ya kubutar da mutane, idan kuma mugu ne ya bi son zuciyarsa ya halaka ya halakar da mutane. Shiyasa ya zama wajibi a fadakar da mutane mugun Malami.

Hawa mumbarin mugun Malami ya fadi laifin shugaba da aibanta shi, koyad da mabiya mugun tunani da tasirantuwa da shi ne, sabanin yi ma shugaba Addu’a ta shiriya da samun nasara saboda mabiya su koya su tasirantu da hakan. Wannan ke nuna cewa Malami kodai ya zama mai koyad da Al-Ummah alheri ko sharri daga maganganunsa akan mumbari ko majalisin karatu.

Idan Malami nagari ne mai Ikhlasi da neman maslaha ma Al-Ummah kuma ba makwadaici ba, kamata ya yi ya je ya yi ma shugaba Nasihah a sirrance ba koya ma mutane aibanta shugaba akan mumbari ba. Idan Malami mai Ikhlasi ne kuma ba mai kwadayi ba, to shugaba komai tsaurin kansa sai ya saurare shi. Fir’auna ma ya saurari Annabi Musa (AS) duk da cewa yana zarginsa da yi masa butulci saboda shi ya raineshi.

Kamar yadda naga an hikayo a shafin facebook cewa: Tsohon Shugaban Kasa Shagari yace: a zamanin mulkinsa duk lokacin da ya je hutu Sokoto, idan aka ce masa ga Sheikh Abubakar Mahmud Gumi (rh) ya zo wurinsa sai gabansa ya fadi, saboda yana yi masa Nasihah akan hakkin da aka daura masa na Amanar Al-Ummah wanda yake saka jikinsa ya yi sanyi. Idan Sheikh Gumi zai tafi ya kawo kyautan kudi ya bashi baya karba.

Wani zai ce ai shugabannin mu na yanzu basa daukan Nasihah kuma kamar Addu’ar shiriya bata tasiri akan su, to matsalar mu ne, domin “kamar yadda kuke haka za’a shugabantar akan ku”. Shugaban nan dai daga cikinmu yake ba daga wani wuri ba. Mafita sai mun gyara, mun yi hakuri kuma mun tsananta Addu’a ba yin bore da tawaye ba.

Mugun Malami hadarinsa tafi ta mugun dan siyasa, domin tasa (dan siyasa) ta duniya ce, takaitacciya ta dan wani lokaci ne a duniyar ma. Fitinar Boko Haram wanda har yanzu ba mu gama fita daga cikinta ba tasirin mugun Malami ne. Duk wanda ya bibiyi yadda Kungiyar Boko Haram ta fara har zuwa inda ta kai, ya tabbata masa cewa daga irin wannan aibanta shugabanni ta fara, na fadan aibunsu da kiransu tagutai a gaban mabiya, har ta kai ga yin bore da daukan makami don su kafa daula tasu ta daidai da adalci. Mun ga irin musifar da yakin wannan kasar ya shiga a sakamakon tasirin wa’azin muyagun Malamai yan Boko Haram, sun bata ma mabiyansu duniyarsu da Lahirarsu, kuma suka haddasa halaka rayukan dubban Jama’a da dukiyoyinsu. Irinsa ne muka sake gani wurin Zakzaky da mabiyansa.

Su ma wadancan ma su shiga rigan malamta suna tuzura Jama’a akan mahukunta, da za su ware su ce za su yi fito-na-fito da Hukuma za’a a sami mabiyan da za su bi su a haifar da fitina da tada zaune tsaye a cikin Al-Ummah.

Kasashe irin su Libya da sauransu da irin wannan mugun wa’azin muyagun Malamai akan mahukunta ne har su ma suka kai halin da suke cikin a yau. Yanzu su gwammace da sun yi hakuri da yin Adduar shiriya ga shugabannin da suka yi ma bore da tawaye da yafi musu.

Bisa wannan ne muka ga ya zama mana wajibi mu fadakar da Al-Ummah mugun Malami dake tunzura Jama’a akan mahukunta wanda yake kai ga haddasa fitina da musifu a cikin kasa.

Wannan shine gaskiyar lamari kuma shine Mazhabar da ni da ire-ire na muke akai na yadda danganta tsakanin shugaba da mabiya yake a mahangan Musulunci da kuma yadda Shari’a ta tsara mu’amalar bangare biyun ya zama.

Wanda ya gamsu Alhamdu lillahi, wanda kuma bai gamsu ba to Allah ya ganar da shi. Mu dai ba za mu fasa yin Nasihah akan yin hakuri da mahukunta da yin Addu’a tagari a gare su ba. Idan kuma wani hakan bai masa ba, to sai ya bar bibiyar mu a wannan kafa ta sada zumunta, illa iyaka kenan

Allah muke roko Ya shiryar da mu da shugabannin mu Ya datar da su, kuma Ya shiryad da masu son tada fitina a cikin Al-Ummah, in kuma ba masu shiryuwa ba ne Ya iyam mana sharrinsu, ameen

Magajin Mallam: Abu Yahya (Aslam)

Mun sami wannan nasiha ne daga shafin sada zumunta na Magajin Malam.

Tags: Abu YahyaAbujaAzumiGumiHausaKadunaKhalilLabaraiLereMagajin MalamMalamaiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESShagarishugabanniWa'azi
Previous Post

Shirin Fadama III zai agaza wa masu gudun hijira 1,840 a jihar Bauchi

Next Post

WATA SABUWA: ’Yan sanda sun gayyaci Saraki kan fashin bankunan Offa

Mohammed Lere

Mohammed Lere

Next Post
Bukola Saraki

WATA SABUWA: ’Yan sanda sun gayyaci Saraki kan fashin bankunan Offa

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi
  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.