• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

‘Yadda sojojin Najeriya da na Kamaru suka rika cin zarafin mata a sansanin gudun jihira’

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 26, 2018
in Labarai
0
IDP in Borno State

IDP in Borno State

Matan da ke zaune a sansanonin gudun hijira bayan sun kubuta daga Boko Haram, sun bayyana yadda sojojin Najeriya da na Kamaru suka rika cin zarafin su.

Matan sun yi wannan bayani ne a Abuja a wani taro wanda Kungiyar Jinkai ta Duniya, Amnesty International ta shirya, domin gabatar da rahoton ta dangane da abin da ya rika faruwa da wanda ke faruwa a sansanonin gudun hijira.

Wasu kalilan da ga cikin matan sun yi jawabai ga ‘yan jarida a wurin taron.

Wata mai suna Kella Haruna, ta ce ta ga bala’i da rayuwar kunci a sansanin gudun hijira.

Ta ci gaba da cewa sojoji da kuma jami’an tsaron hadin-guiwa sun rika cin mutuncin mata.

Kella wadda ta yi magana cikin harshen Kanuri, ta ce an yi lalata da mata sosai, sannan wasu kuma idan su na so a ba su abinci, to sai sun yarda sun bada kan su an yi lalata da su.

Kella ta ce daga garin Banki ne aka kubutar da su bayan da Boko Haram suka mamaye su.

“Daga nan da aka tura mu cikin Kamaru, mun ga cin zarafi da tozartwa matuka. Domin tsirara suka sa muka yi, haka sojojin kasar suka bar mu kwana hudu babu ko abinci.Haka suka sake maida mu Banki.’’

Kella ta ci gaba da cewa ta tabbatar da mazan su na nan, to babu yadda za a yi su fuskanci cin zarafi da tozartawar da aka yi musu.

“Mu na a Bama ne aka zo aka kama mazajen mu, aka daure musu idanu, aka loda su a cikin mota aka nufi Maiduguri da su. Amma aka ce mana za a kai mu inda mazajen na mu suke, amma kuma har yau din nan babu labari.

“Sojoji suka ce ina matan nan, ku zo za mu kai ku inda mazajen ku suke. Daga nan muka dan tattara komatsan da suka rage mana, muka fito. Suka dauke mu amma duk suka jibge mu a dai cikin Bama din a wani sansanin da ke asibitin garin.

“Maganar gaskiya a sansanin Bama inda nan ne asibitin garin a da, babu maganar abinci, idan ka yi magana kuma su yi ta jibgar ka. Kuma sojoji sun rigaya sun kwace duk kudaden da ke hannun mu. Suka bar mu biyu.”

Daga nan ne kuma inji Kella, sojojin suka fara bibiyar su, wadda suka ga ta yi musu, sai su nemi sai sun yi lalata da ita.

Wata mai suna Fatima Bukar, ta bayyana yadda sojoji suka kame mijin ta, ‘ya’yan ta da ‘yan uwan ta maza.

Ta ce har yau babu wanda ya ce mata ga inda aka tsare su tun da aka kame su aka tafi da su.

“Kafin ma su dauke su daga can su canja musu wuri, sai da suka fito da su, suka yi musu wanka, sannan suka loda su zuwa Maiduguri.’’

Sojoji sun sha cewa wadanda ake kamawa din ana damke su ne domin a bincika a gane shin ‘yan Boko Haram ne ko kuwa ba su ba ne.

Wasu daga cikin wadanda ake kamawa din ana sakin su idan aka gano cewa ba Boko Haram ba ne. Amma kuma da yawa na can a kulle har yau ba a gurfanar da su an yanke musu hukunci ba, su na tsare a hannun sojoji.

YAKAMATA GWAMNATI TA SHIGA LAMARIN

Hamsatu Allamin, wadda ta kafa Allamin Foundation domin dawo da zaman lafiya a Jihar Barno, ita ma ta yi magana a wurin taron inda ta nuna takaicin yadda sojoji da jami;an tsaron na Vigilante suka rika tafka lalata da matan.

“Kai ko ma da soja daya ne tal ko dan CJTF daya ne ya yi wa mace daya fyade, to fa tilas sai an hukunta shi. Duk da cewa yawancin wadannan matan su na tsoron su fito su yi magana saboda tsoron kada wani abu kuma ya biyo baya.

Allamin ta ce an ci zafin mata akalla 1, 600 abin da ya hada har da duka. Ta ce maza akalla mazaje 437 sun bace daga sansanoni

“Ai har gara ma Boko Haram da wasu sojojin. Ba ina magana ne a kan daruruwa ba, sai dai na ce dubbai. Ya kamata a fara ganin canji a fadin kasar nan. Ina fatan hukumar sojoji ba za ta ji haushin wannan ba. Amma ta nemo hanyar magance wannan matsala.

Daraktan Kare Hakkin Wanda aka Zalunta a Hukumar Kara ‘Yancin Dan Adam, ya tabbatar wa Premium Times cewa sun karbi koke-koken cewa akwai mazaje 437 da har yau ba a san inda suke ba.

“Na rubuta wa sojoji takarda, amma sun maido min cewa babu ko daya daga cikin jerin sunayen wadanda ake nema din da ke tsare a hannun su a jihar Barno.

Ita kuwa Sa’adatu Mahdi, daya daga cikin wadda aka kafa ‘Bring Back Our Girls da ita, cewa ta yi bala’in da ake fama da shi a yankin Arewa maso gabas, ya wuce tunanin kowane bil Adama.

“Ai lokacin da aka kama daliban Dapchi, mun rika tuntubar Boko Haram da ba su dauke da makamai, su kuma su na tuntubar fitinannun na su. Da aka tsagaita wuta, ai cikin sati daya suka dawo da daliban bayan an tsagaita wutar.

“To idan har za a iya kulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta sati daya, don me ba za a kulla tsagaita wuta ta daina yakin gabadaya ba, yadda za su fito a daina yakin haka nan?”

Da yake jawabi, shugaban Kwamitin Mashawartan Kungiyar ta Jinkai, Auwal Rafsanjani, ya ce kungiyar ta su ta na taimakawa ne domin jama’a su fito su san ‘yancin su.

“Kungiyar Jinkai ta Kasa da Kasa ba ta fito ta na gasa da kowane bangare ba ne. kawai ita ta na aiki ne domin tabbatar da cewa ana kare wa kowane dan Najeriya ‘yancin sa.”

“Ganin irin hujjojin da muke da su ne ya sa muka kawo wasu daga cikin wadanda aka ci wa zarafin domin a ji daga bakin su,

“Don me wasu za su rika cewa mu na kokarin rikita Najeriya? Mu fa mu na nuna wa gwamnati ne cewa ta fito ta yi abin da ya dace ta yi wajen kare hakkin ‘yan Najeriya.”

‘YAN MAJALISA SUN CE WANI ABU

Sani Zorro, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Tarayya a kan Sansanoni da ‘yan gudun hijira, ya ce duk ta inda aka buga aka buga, to ana daina yaki ne ta hanyar sasantawa.

“Tunda dai mun kasa ganin karshen wadannan Boko Haram a cikin sama da shekara biyar, to ya kamata a samu wata hanyar kawo karshen wannan fitina.” Inji Zorro.

“Shin wai ku na tsammanin kashe-kashen da ake fama da su a jihar Kaduna da Zamfara duk ba su da alaka da Boko Haram ne? Ai yanzu Najeriya ta na takara ne da kasar Syria wajen fattatakar jama’a daga matsugunan su.”

Shi kuwa Sanata Shehu Sani, cewa ya yi bai kamata gwamnati ta yi watsi da rahoton Kungiyar Jinkai ta Duniya ba.

“Ana yawan cin zarafin mata, kuma wannan abin takaici ne. kuma wannan rahoto bai dora wa gwamnati laifi ba, abin da ake fama da shi ne a kasar nan.

Ya ce abin takaicin kuma shi ne jami’an gwamnati ba su ma tsaya sun karanta rahoton ba, saboda hankalin su kawai ya karkata ga zabe, sai suka fara bobbotai kawai.

“Idan dai har gwamnan da ke kan mulki a yanzu ba kunya ba tsoron Allah har ya ce wai kashe-kashen da ake yi a Arewa duk zuguguta shi ne ake yi, bai taka kara ya karya ba, to ana cikin mummunan matsala fa.”

Tags: Boko HaramHausaHausa Premium TimesLabaraimata
Previous Post

Buhari ya soke kwangilar makaman Isra’ila ta dala miliyan 195 wadda Ameachi ya bayar

Next Post

Madrid ta zama zakaran kungiyoyin kwallon kafa na nahiyar Turai a karo na uku a jere

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Mohammed Salah

Madrid ta zama zakaran kungiyoyin kwallon kafa na nahiyar Turai a karo na uku a jere

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘARYAR CBN TA ƘARE: Tinubu ya dakatar da Emefiele, gogarman da ya yi wa Naira fentin zabibi, bayan dala ta kai Naira 750 a ƙarƙashin sa
  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.