• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BOKO HARAM: Ni da komawa Konduga har abada – Wata mai ‘ya’ya takwas

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 9, 2018
in Labarai
0
BOKO HARAM: Ni da komawa Konduga har abada – Wata mai ‘ya’ya takwas

Hansatu Koduga

Hansatu Mustapha, mace ce mai shekaru 36, ta kasance ba ta da wani zabi sai matawa da garin su Konduga, garin da Boko Haram su ka fatattaka, gaba daya al’ummar garin suka fashe zuwa cikin Maiduguri, kamar shekaru uku da suka gabata.

Matar mai ‘ya’ya takwas, ta na cikin ‘yan kalilan da suka samu kubuta gaba dayan su. Domin ba ta rasa ‘ya’ayan ta ko guda daya ba, sai dai kuma ta yi asarar komai a garin Kodunga.

“Mu na cikin zaman jin dadi da kwanciyar hankali da miji na da ‘y’ayn mu a Konduga, kusan shekara 20 da yin aure, sai Boko Haram su ka kai mana mummanan hari. To a nan ne na tabbatar da rudin kai na da nake yi, na ce ashe dai mafarkin da na ke cewa Konduga ta fi ko’ina dadin zama a duniya, duk mafarki ne, ba gaskiya ba ne.

“A halin yanzu ba ni da komai, ba ni da kowa sai yara na da na ke kula da su.”

“Kwata-kwata garin Konduga, inda can ne mahaifa ta, ya fita daga raina gaba daya. Garin da Boko Haram suka kashe min miji na aka bar ni da marayu, me zan yi da shi, ga shi kuma ba ni da sauran komai a ciki.

Garin Konduga dai ya sha fama da hare-haren Boko Haram, amma ba su yin nasar saboda tashi-tsayen da sojoji suka rika yi a lokacin su na hana su kutsawa. Amma a ranar da suka yi galabar shiga garin, a ranar kowa ya ji a jikinn sa. A ranar da suka an yi bata-kashi sosai.

A cikin garin Kwanduga ne a watan Satumba, 2014 sojoji suka ce sun kashe Abubakar Shekau. Amma daga baya aka gano cewa ba gaskiya ba ne, wani dai ne aka kashe mai kama da shi.

Da Boko Haram sun yi nasarar karbe Konduga a lokacin da su ke zabari da kumajin kai hare-hare barkatai, to kuwa da sun samu saukin kai wa Maiduguri mummunan hari, ko kuma su kwace Jami’ar Maiduguri, wadda ke wajen gari, kan hanyar zuwa Bama.

Amma lokacin da Boko Haram suka samu gabalar shiga Konduga, a lokacin karfin su ya ragu sosai, ba su da namijin kusarin tunkarar Maiduguri, kuma daidai lokacin an damfare sojoji jingim a babban birnin na jihar Barno.

A yayin harin da suka kai wa Konduga, wanda yay i sanadiyyar al’ummar ganin fashewa kowa ya tsere, Hansatu ta ce mijin ta ya ji mummunan rauni, amma yay i ta-maza shi ma ya gudu daga garin, duk kuwa da irin mummunan halin da ya ke ciki.

“Kafin mu kawo kan mu Maiduguri, sai da muka shafe kwanaki uku mu na ta walagigi a cikin daji. Da muka zo, to mun yi sa’a Bulama na Modusulumri ya san miji na. Sai ya ba mu daki daya, inda ni da miji na da ‘ya’yan mu takwas mu ke kwanciya a ciki.’’

RAYUWAR HANSATU BAYAN BA MIJI

Hansatu ta kasance ita ce maigida-kan-gidan ta, domin mummunan ciwon da mijin ta ya ji sanadiyyar harbin bindiga da aka yi masa shi ne sanadiyyar ajalin sa.

“Duk da ciwon da miji na ya ji daga harbin da Boko Haram su ka yi masa, haka ya yi ta gaganiya na fadi-tashin ciyar da mu, har ajalin sa bayan shekara uku da harbi. Daga nan fa ne duniya ta yi min kunci da duhu, saboda an bar ni da nauyin yara takwas a gaba na.

“Tsayawa ma ina bada labarin irin wahalar da mu ka shiga, shi kan sa wata wahalar ce mai zaman kan ta.

Ta ci gaba da cewa su da a can baya su ke rayuwa cikin rufin asiri da wadata, sai ga shi sun koma rayuwar kaskanci, wulakanci ta katutun fakirancin da abinci ma ba ka san lokacin da za ka gani ba, balle a ba ka har ka ci.

“A haka muka rika rayuwa a cikin dogaro da dan abin da makwauta za su ba mu mu ci, wadanda su din ma mabukata ne, ba wadatar gare su ba, domin idan aka ba su dan abin da suke ba mu, su ma karba za su yi.” Inji Hansatu.

“Haka na rika fita kwararo-kwararo, gida-gida ina neman aikatau; a matsayi nan a uwa da ke da yara takwas a gaban ta, cikin su har da matasan ‘yan mata, na hana ‘yan matan cikin su fita waje neman aiki, don gudun kada a bata su. Saboda na ga irin yadda maza marasa imani ke amfani da talaucin mata ‘yan gudun hijira sun a bas u dan abin duniya kalilan sun a lalata da su don su samu na sayen abinci. Wasu kuma su ciyar da iyalin su.

“Duk ranar da na fita ina aikatau a gidaje kamar wankin kayan matar gida da na yaran ta kanana da wanke-wanke, na sha fama da musgunawa da cin zarafi, amma sai na danne zuciya ta, saboda na fita ne neman abin da iyali na za su ci.

MAHAKURCI MAWADACI

“Ba mu samun sukunin rayuwa ba sai da shekara uku cur ina gaganiya a cikin kaskanci, sai wata rana wata kungiyar bayar da tallafi ta kasar Norway, (Norwegian Refugee Council), su ka zo unguwar mu sun a daukar wadanda za su yi wa horon koyon sana’o’i.

“Ni da wasu mata aka koya mana yadda za mu yi kananan sana’o’I, kuma aka ba kowanen mu N43,500 kyauta domin mu ja jarin yin sana’ar duk da nag a zan iya yi.” Inji Hansatu.

Dalilin wannan ne yanzu Hansatu ta samu sukuni, ta daina fita yawon nema, ta kama sana’a kuma ta na samun nasibi. Ta ce yanzu dukkan yaran ta sun a zuwa makaranta, kuma jari da na kara habbaka.

NI DA KONDUGA HAR ABADA

Cikin watan da ya gabata ne Gwamnatin Jihar Barno ta yi shelar maida ‘yan gudun hijirar Bama zuwa gida domin ana kan aikin sake gina garin da gwamnatin jiha da ta tarayya key i.

Garin Konduga ya na kilomita 37 tsakanin sa da Bama, daga Maiduguri. Wato kenan tunda jama’ar Bama za su iya komawa gida, su ma na Konduga kenan za su iya komawa.

Akwai mutane kalilan a yanzu da ke zaune a sansanin Konduga. Amma dai akasarin mutanen garin duk sun fashe.

Amma wannan labarin komawa gida, sam bai faranta wa Hansatu rai ba, cewa ta yi ma it aba za ta koma ba.

“Na sha azaba, na rasa komai a garin. Me zan koma kuma na yi a Konduga. Ni fa ko mafarkin komawa garin nan ban a fatan na kara yi, sannan ko tuna garinn nay i sai fargaba ya kama ni. Me zan koma na yi a garin da ba ni da kowa, ba ni da komai?

“Dan uwan da kawai na ke da shi a Konduga, shi ne miji na, kuma yam utu. Shin idan ma na ce zan koma, to a gidan wa zan zauna? Ni yanzu na yanke shawarar rayuwa a cikin Maiduguri, inda a nan na fi jin cewa rayuwa ta ba ta tattare da wata barazana. Kuma b azan sake yin fatar sake jefa yara na cikinn wani garari ba.

“Masu cewa na koma ai bas u san irin wahalar da muka sha a daji har kwanaki uku kafin mu kawo kan mu Maiduguri daga Konduga ba.

Hansatu ta ce akwai wadanda su ka fi ta shan azaba sosai, wadanda har yanzu babu mai taimaka musu.

“Amma mu a nan unguwar Modusulumri an ba mata 200 kowace naira 43,500 kyauta, domin yin kananan sana’o’i. amma har yanzu akwai wadanda ke fama da rayuwar kunci.”

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar da cewa akwai sama da ‘yan guun hijirar Boko Haram da ke cikin Maiduguri da kuma cikin sansanonin ‘yan gudun hijira.sai dai rahoton ya kara da cewa, mutane 230,000 ne kadai ke zaune a sansanoni daban-daban.

Sauran kuma kamar yadda rahoton ya nuna, duk sun a cikin gari a gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki. Kena kimanin miliyan 2.7 ne warwatse a cikin jama’a.

Tags: AbujaBoko HaramHansatuHausaKondugaLabaraiMaiduguriNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Majalisar Tarayya za ta binciki almubazzaranci da kudaden aikin killace makarantun Arewa-maso-gabas

Next Post

Dalilin da ya sa nayi watsi da gayyatar majalisa – Sufeto Janar, Ibrahin Idris

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Ibrahim Kpotun Idris

Dalilin da ya sa nayi watsi da gayyatar majalisa - Sufeto Janar, Ibrahin Idris

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki
  • TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna
  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar
  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama wasu 161 a cikin makonni biyu a yankin Arewacin Najeriya
  • Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.