Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan, ta bayyana cewa ta gano Babban Jami’in Diflomasiyyar Najeriya da aka kashe a Kahartum, babban birnin kasar.
An bayyana sunan sa Habibu Almu, kuma ma’aikacin Hukumar Shige-da-fice na a nan Najeriya, wanda aka tura aiki a ofishin jakadancin Najeriya da ke kasar Sudan.
NAN ta ruwaito labarin kashe Almu, inda ta hakaito cewa a soshiyal midiya an ce an yi amfani da wuka wajen kashe shi a cikin gidan sa.
Ma’aikatar Harkokin Waje ta Sudan, ta nuna takaicin kashe shi da wasu suka yi, kuma ta ce gwamnatin Sudan ta na ta tsaurara bincike domin gano makasan.
Discussion about this post