Shugaba Muhammadu Buhari ya gana da ‘yan wasan kwallon kafa ta Kasa Super Eagles, a safiyar Laraba.
Wannan dai ziyara ce na yi wa shugaba Buhari sallama a shirin su na tafiya kasar Rasha domin fafatawa a gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya da za a fara ranar 14 ga wannan wata na Juni.
Kafin nan, Super Eagles din za su buga wasar sada zumunta da kungiyar kwallon kafa ta kasar Ingila ranar Asabar mai zuwa.
Discussion about this post