Kungiyar Koli da ke kula da harkokin addinin Musulunci NSCIA ne ta sanar da ganin watan, in da tace gobe ne 1 ga watan Ramadan.
Bayan haka sarkin Musulmai Abubakar Sa’ad ya sanar da ganin watan a jihohin Sokoto, Niger, Yobe, Port Harcourt, Borno, Gombe, Jigawa da wasu wurare da dama.
Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wa musulmai fatan Alkhairi da yin Ibada karbabbiya.
Discussion about this post