Duk da amincewa da a sake zaben sabbin shugabannin jam’iyyar APC da jam’iyyar ta yi, Gwamnan jihar Adamawa Jibirilla Bindow ya ce shi ba za a yi sabon zaben shugabannin jam’iyya a Jihar sa ba. Na shi shafaffu da mai ne.
Jibirilla ya bayyana haka ne a lokacin da shugabannin jam’iyyar ta jiha suka kawo masa ziyara fadar gwamnati dake Yola.
Idan ba a manta ba, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci jam’iyyar ta gudanar da zabukkan kujerun shugabannin jam’iyyar na kasa da jihohi baki daya.
Jibirilla ya ce babu zaben da za ayi a jihar, cewa dukkan su a jihar suna nan daram dam a kujerun su.
” Wadanda za mu canza sune wadanda suka rasu amma duk wanda yake kai yanzu ya ci gaba da zama abin sa a kujerar sa.
Gwamna Bindow ya ce shi dama can yana tare da wadanda suke bayan kada a sake zaben shugabanni a jam’iyyar APC yanzu. A jihar sa ta Adamawa kuwa, babu wanda zai sauka da ga kujerar sa domin ” babu zaben da zan yi.” Inji Bindow.
Yanzu dai jam’iyyar na cikin wani irin sarkakiya ce domin har yanzu kan ‘ya’yan ta sun rabu game da zaben.
Discussion about this post