A ranar Lahadi ne gwamnatin tarayya ta yi kira ga mutane da a daina Zubar da Ledoji da fasassun robobi a ko-ina cewa hakan na lalata wuraren zaman mu ne da muhallin mu.
Ministan muhalli Ibrahim Jibril ya bayyana da haka a Abuja a taron kare muhalli wanda ake yi ranar 22 ga watan Afrilu na kowane shekara.
Jibril ya bayyana cewa hakan na lalata muhalli sannan yakan zamo illa ga lafiyar mu.
Discussion about this post