Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara Mohammed Shehu ya sanar cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane uku a kauyen Bawan Daji dake karamar hukumar Anka a jihar.
Shehu ya sanar da haka ne ranar Laraba inda ya kara da cewa maharan sun kai hari kauyen ne da safiyar Laraba.
Ya ce a daidai maharan na aikata wannan mummunar abu ne wasu mazaunan kauyen suka kira jami’an tsaro.
” Mun kora su a arangamar da muka yi sannan da yawan su sun tsere da raunin harsashin bindigogin mu.”
A karshe Shehu ya yaba wa mazauna wannan kauyen sannan ya ce su gaggauta sanar wa jami’an tsaro duk wanda suka ji an kai shi asibiti dauke da raunin bindiga.
Discussion about this post