• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda Saraki ya samu zama daram a Majalisar Dattawa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
March 22, 2018
in Rahotanni
0
Yadda Saraki ya samu zama daram a Majalisar Dattawa

Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Bukola Saraki, ya samu nasarar hayewa kan kujerar mulkin majalisa, a wani yanayin kutunguila da algungumacin siyasa. A gefe daya kuma, hawan sa shugabancin bai yi wata-wata ba, sai ya nuna salon mulkin dannau zai yi, duk wanda ya danne ko ya take, to ya taku kuma ya dannu.

Da ya ke ya iya tuggun siyasa, kamar mahaifin sa, marigayi Olusola Saraki, wanda shi ma ya yi shugabancin Majalisar Dattawan a Jamhuriya ta biyu, lokacin mulkin Shehu Shagari, sai ya kasance abin kamar a nono ya sha – wato abin nan da Bahaushe ke cewa, ‘barewa ba ta gudu dan ta ya yi rarrafe. (Premium Times Hausa)

Bai wani bata lokaci ba, sai ya fara nuna maitar sa a fili, tun ya na yi a boye, Saraki ya jaddada mulkin ‘yan karambosuwa da karfa-karfa. Ya yi haka domin gwanin kitimirmirar siyasa ne, ta yadda ya gina doguwar katanga ya kange Majalisar Dattawa daga Jam’iyyar APC da Shugaba Muhammadu Buhari, yadda ko leken cikin ta ba su iya yi, ballantana har su jefa kafa ciki su rika yi masa katsalandan.

Ya nuna cewa shi dattijon da ya iya fadan gurugubji, wato fada da tsarar sa dattawan jam’iyya, shugaban kasa da duk wani kushegeren mamba na majalisar dattawa. Fadan dattawa ba a kuka ko zubar da hawaye, sai dai wanda ya ji naushi a hanci ya fyace. Shi kuwa Saraki hatta rugumutsin da ake ta tafkawa da shi a gaban alkali, bai taba yin ko gezau balle ya fyace ba. Jure dafi sai bauna!

Sanatoci uku da su ka nemi lakutar masa hanci da yatsu, tun ba su kai ga cewa kulle ba, ya karya musu yatsu, tilas su ka saduda. Saraki ya nuna Majalisar Dattawa cewa shi fa gwangwala ce, a hau ki a zame, ki hau mutum ki zauna daidai.

Irin karankatakaliyar da kamtsa kafin ya zama shugaban majalisar dattawa ta isa a yarda cewa Saraki goga ne mai nike wa shanu turba – ka na gaba shanun ka biye.

Duk wata kisisina da kullen-kullen sai Sanata Ahmed Lawan ya zama Shugaban Majalisa, hakan bai yi nasara ba kamar yadda shugabannin jam’iyyar APC su ka nemi yi. Yayin da aka baje kujerar a faifai aka daka wasoso, sai ga tsokar naman gaba dayan ta a cikin bakin Bukola Saraki. Gafiya tsira da na bakin ki!

Bayan kura ta lafa aka duba aka ga Ahmed Lawan da shi da magoya bayan sa ko kasusuwa ba su samu ba. To Saraki dama rikakken dan kokawa ne, amma duk da haka a wannan ranar sai da ya hada da sojan-haya, Ike Ekweramadu, ya samu ya yi musu mai shal.

Ba da dadewa ba Saraki ya zame wa majalisa karfen kafa, ta yadda ko ta ina aka motsa, ba a maganar kowa sai maganar sa. Babu wani batu, mai dadi da maras dadi, sai batun da ya shafi Saraki. (Premium Times Hausa)

A bangare daya kuma, duk wani kokarin a tube shi an yi, ba a yi nasara ba. An maka shi kotu, har yanzu shiru. An tayar masa da cida mai rugugi, amma ko razana bai yi ba, balle ya gudu ya shige daki, kada aradu ya fada masa.

BARDE BA A HAYE MAKA:

Hawan sa shugabancin majalisa bai yi wa shugabannin APC dadi ba, musamman uban tafiyar jam’iyyar, Bola Tinubu. Babu abin da Tinubu bai yi ba, domin ya tabbatar an sake zabe, an kayar da Saraki, amma ko kusa ba labari.

Da ya ke Saraki mai wayau ne, yayin da ya cika bakin sa da tsokar naman da ya raruma a tsakiyar majalisa, sai ya rika cizga ya na samma zaratan da suka taya shi kokawa. Haka ya rika ba ‘yan-gaban-goshinsa mukaman shugabancin kwamiti-kwamiti masu romo da kuma bargon tsotsa. Ko ka na APC ko PDP, matsawar ka taya shi fizgar nama, to kai ma sai an ci tare da kai.

Haka aka rika tafiya, Saraki ya zama duwawu, dole gwamnatin APC ta zauna da shi. A matsayin sa na mutum mai mukami na uku a Najeriya, bayan Buhari da Osinbajo, sai Saraki ya zama abin da Hausawa ke cewa, ‘tilas a ci kasuwa tare da makiyi.’ Haka za a rika haduwa a wurin taro ko fadar gwamnati ana kallon-kallo tsakanin Shugaban Kasa da Shugaban Majalisar Tarayya.(Premium Times Hausa)

Ba a nan ya tsaya ba, sai da ya tabbatar da cewa babban gogarman sa, Sanata Ali Ndume shi ne ya zama Shugaban Masu Rinjaye. Sai dai kuma Ndume ya gamu da gamon sa a lokacin da ya zakalkale wa Saraki, ya nemi Majalisa ta yi bincike kan wani rahoto da ke da nasaba da batun kin amincewa da shugaban EFCC, Ibrahim Magu.

YADDA YA DAMALMALA NDUME

Yayin da Ndume ya fito karara ya nuna goyon bayan sa ga shugaban riko na EFCC, Ibrahim Magu, wanda suka fito daga jiha daya, nan take ya raba hanya da Saraki da ‘yan-karankatsagallin Saraki. Kura ta tirnike, har aka tsige Sanata Ndume daga Shugaban Masu Rinjaye, aka nada Ahmed Lawal.

An yi wa Ndume bi-ta-da-kulli yayin da ya tsoma bakin sa a sha’anin zargin Saraki bai bayyana yawan kadarorin sa ba, inda ya ce jaridu sun nemi a binciki Saraki. Wannan ya kai ga an dakatar da Ndume daga majalisa, kuma tilas ya hada kayan sa ya fice.

ISHARA GA ABDULLAHI ADAMU

Daya daga cikin karin karfin da Saraki ya samu a majalisa shi ne kyakkyawar alakar sa da sanatocin da a baya sun taba yin gwamnoni kamar sa kenan. musamman ma Sanata Abdullahi Adamu, tsohon gwamnan jihar Nassarawa, wanda Saraki kan kira shi ‘yayana’, ko kuma ‘uban kasa.’

Duk wannan dadin bakin bai hana Saraki wasa zarto ya gigara wa kujerar da Adamu ke takama da ita, ta shugaban kungiyar Sanatocin Arewa ba, a lokacin da ya nemi ya shige wa Saraki hanci.

Adamu ya nuna rashin amincewa da gya dokar zabe, shi da wasu gungun sanatoci, su na cewa makarkashiya ce ake so a yi wa Buhari. Wannan rudani ya janyo an yi wa Adammu terere a duniya, inda aka ce an tsige shi saboda ya ci kudin kungiya har naira milyan 78, wadanda ya ce wai a gona ya boye su, amma wasu birai suka yi watandar kudaden gaba dayan su. (Premium Times Hausa)

A halin yanzu an shata layi, Adamu ya zama cikakken dan adawar kokarin taka wa Saraki burki. Tuni dai ake kallon Adamu ba zai iya jure karo-da-karo da Saraki ba, domin a ganin wasu, kahonnin sanatan ko kadan ba su kai na Saraki kwari ba.

TAKA WA OVIE OMO-AGEGE BURKI

Sanata Ovie Omo-Agege na daya daga cikin sanatoci 9 da suka yi wa Saraki tawayen kin amincewa a sauya ranakun zabe. Ya fito ne daga shiyyar tsakiyar jihar Delta. Ya tashi ya nemi a ba shi damar yin magana, amma Saraki ya nuna masa ya zauna ya yi wa mutane shiru. Danganta sauya ranakun zabe da makarkashiya ga shugaban kasa da su Omo-Agege suka yi, ya janyo masa tsangwama da dora masa karan-tsana.

Kwanaki kadan sai Dino Melaye ya yi nuni da wani jawabi da Omo-Agege ya yi, ya nemi a yi bincike, kuma aka amince kwamiti ya binceke shi.

DINO MELAYE: GOGARMAN SARAKI

Sanata Dino Melaye ne a sahun gaban goyon bayan Saraki duk rintsi. Ko kotu Saraki zai je, bai taba barin Melaye a gida ko a ofis ba. Ko lokacin da EFCC su ka gayyaci Doyin, matar Saraki, Melaye ne babban dan rakiyar ta. (Premium Times Hausa) Baya ga wannan, Melaye ne kanwa-uwar-gamin da ya shugabanci kwamitin binciken Sanata Ndume, kuma shi ne a sahun gaban kitsa yadda aka tsige Abdullahi Adamu daga shugabancin kungiyar Sanatocin Arewa.

Tags: AbujaAdamu AbdullahiDinoHausaLabaraiNajeriyaOlusola SarakiSaraki
Previous Post

Kungiyar Likitoci ta Kasa ta kirkiro baji don bambamta kwararrun likitoci da baragurbi cikin su

Next Post

Mai unguwa a Jigawa ya kori wasu makiyaya don basu bashi ladar zama a kauyen Gwaram

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
An zargi wasu makiyaya da kashe Sufeton ’Yan Sanda a Jihar

Mai unguwa a Jigawa ya kori wasu makiyaya don basu bashi ladar zama a kauyen Gwaram

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju
  • Kotu ta tsige Kori Sufeto Janar din ‘yan sandan Najeriya Usman Baba, ta ce zaman sa IG ya haramta bisa doka
  • Diezani ta maka EFCC da Ministan Shari’a kotu, ta na neman diyyar naira biliyan 100, saboda sun kira ta ‘ɓarauniya’
  • Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje
  • JAWABIN BANKWANA: Na gama da ku lafiya, inda na gaza kuma a yayyafe – Buhari

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.