Bayan duba bayanai da ga hukumomin tsaron Najeriya, Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai ziyarci jihohin Zamfara, Benuwai, Ribas, Taraba da Yobe domin gani wa Idanuwar sa irin halin da mutanen jihohin suka shiga sanadiyyar rashin zaman lafiya da yayi musu katutu.
A wata takardar sanar da haka da ya fito daga fadar shugaban Kasa, Buhari zai fara wannan ziyarar ce daga yau Litini.
Zai fara daga jihar Taraba ne inda zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma ya gagara.
Discussion about this post