Rundunar ‘yan sadan jihar Jigawa ta sanar wa manema labarai cewa ta yi ram da ‘yan fashin da suka shiga gidan mataimakin gwamnan jihar Abubakar Hadejia.
Rundunar ta bayyana cewa ‘yan fashin sun yi fashi a gidan Hadejia ne ranar Lahadin da ta gabata.
Binciken da suka gudanar ya nuna cewa ashe ‘yan fashi ‘yan sanda ne da ya hada da wani sajen da kuma wasu su uku.