Gwamnatin jihar Kaduna ta kara wa malaman jihar kashi 32.7 bisa 100 na albashin su. Za a kara wa malamai da ke karantar wa a birane kashi 25.2 bisa 100 sannan a kara kashi 5 bisa 100 wa wadanda za a tura wajen gari.
Jaafaru Sani ya ce za a saki sunayen wadanda aka dauka aiki cikin malaman da suka rubuta jarabawar gwaji, 10,000 cikin sama da 36 da suak rubuta jarabawar sannan za a fitar da inda aka tura su nan da makonni biyu masu zuwa.
Discussion about this post