• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

MARMARA CI KAN KI DA KAN KI: Yadda hukumomin tsaron Gwamnatin Buhari ke gurgurar junan su

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 16, 2018
in Rahotanni
0
Lawal Daura

Lawal Daura

Mutane a zahiri na kallon yadda jami’an hukumomin tsaron gwamnatin Muhammadu Buhari ke kazar-kazar, karakaina da kamo wannan, cafko wancan, duk a kokarin su na cika-aikin gudanar da tsaro ga gwamnatin Buhari, ashe ba a sani ba a tsakanin su babu komai daga yankan-baya sai cin-dunduniya sai kuma karo-da-karo, musamman tunda dukkanin su manyan raguna ne.

PREMIUM TIMES HAUSA ta kawo muku irin yadda NIA, SSS da EFCC ke karo da juna a cikin duhu, yayin da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Abba Kyari da ubangidan jami’an tsaron, Janar Monguno ke hararar juna a cikin haske ko a duhu. Wane damu Daura shugaban SSS ke damalwalawa? Me ya sa Magu ya zame wa wasu ogogin sa kadangaren bakin tulu? Ku biyo mu ku ji komai…

NIA: Yadda Aka Yi Wa Mohammed Dauda Dungun-kuturwa:

Tsohon Daraktan Riko na Hukumar Tsaro ta NIA, Mohammed Abba ya tashi da safiyar 9 Ga Janairu, 2018, a cikin nishadi da jin kan sa a matsayin wani babban jigo daga cikin jigajigan jami’an tsaron kasar nan. Ya shirya tsaf domin a ranar ce zai yi taron sirri na farko, shi da Shugaba Muhammadu Buhari, tun bayan da aka dauko shi daga Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Chadi, a cikin Oktoban da ya gabata.

An kira shi a wancan lokacin ne aka ce ba shi rikon hukumar tsaro ta NIA, wacce akasarin ayyukan ta duk leken asiri da kwakule-kwakule ne.

Idan ba a manta ba, tun cikin watan Afrilu da ya gabata ne hukumar NIA ta jefa kanta cikin barankyankyama da harkallar wasu kudi har dala miliyan 43, wadanda aka busa wa usur, aka gano a wani gida an kimshe su, a cikin unguwar Ikoyi da ke Lagos. Fallasa wadannan kudade ya janyo dakatar da shugaban hukumar na lokacin, Ayodele Oke.

Mu koma kan Dauda. A lokacin da ya fito daga ganawa da Shugaban Kasa, an ga fuskar sa cike da annashuwa da fara’a da cika ido, kai da ganin sa za ka yi tsammani ko albishir aka yi masa cewa an nada shi cikakken shugaban NIA, ya tashi daga shugabancin riko.

WANE NE DAUDA?

Wani kwararren jakadan huldar diflomasiyya ne da ke da kwarewa a fannin zakulo boyayyun masu laifin daka-dakar kudade. Majiya ta ce irin yadda ya san kabli da ba’adin masu tuggu, ya cancanta ya rike mukamin shugabancin NIA. Ga shi kuma dama a zaman sa Chadi, babu daren da jemage bai gani ba a rikici da siyasar diflomasiyyar yakin Boko Haram.

Aikin Dauda duk ya na a karkashin ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara a Fannin Tsaro, Babagana Munguno, wanda shi da Dauda din duk kabilar Kanuri ne. Sai dai kuma inda sakar ta cukurkude wa Dauda, majiya ta ce Munguno bai san za a dauki Dauda aiki ba, kuma babu wanda ma ya tuntube shi kafin a dauki Dauda aikin shugabancin NIA. Ashe kenan tilas Dauda ya rika taka-tsantsan kada garin gyaran gantsarwa ko doro, ya karya kugu.

Kwatagwangwamar SSS, EFCC DA SOJOJI:

Kwatsam a safiyar Laraba, 10 Ga Janairu, 2018, kwana daya bayan ganawar Dauda mai rikon shugabancin NIA a lokacin da shugaban kasa, sai yaran Lawan Daura, wato SSS suka shiga Defence Hause da ke Maitama, da nufin wai su na son ganin Abba Kyari, Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa.

Su ka ce sun je ne domin su kare Kyari daga wani kamu da Shugaban EFCC, Ibrahim Magu ya turo jami’an sa su kama Kyari din.

Majiya mai tushe ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa Shugaban SSS Lawan Daura ne da kan sa ya tura jami’an sa da umarnin cewa kada su sake su bari EFCC su kama Abba Kyari.

HARKALLAR NNPC: Ruwa Ba Ya Tsami Banza

Idan ba a manta ba, a farkon watan Oktoban da ya gabata, an fallasa wata cukumurda a kamfanin mai na NNPS, inda aka gano cewa an karkata wasu zunzurutun kudade har naira bilyan 50 zuwa cikin wasu asusu biyar da ke wasu bankuna biyar. Wannan kuwa a zahiri an karya doka, domin a ka’ida, a cikin Asusun Bai Daya (TSA) na gwamnatin tarayya ya kamata a zuba kudaden.

Wannan kakuduba ta kusa yi wa sunan Abba Kyari da mutuncin sa mummunan dameji, domin an ce shi ne ya bayar da umarnin a karkatar da kudin daga Asusun Bai Daya, TSA.

Masana kundin tuggun siyasar Abuja sun gutsuro mana cewa ofishin Shugaban Kasa da kuma ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara a Fannin Tsaro, Munguno, sun damu da wannan kakuduba ta naira bilyan 50 a NNPC, har ma su ka cunna EFCC a wurin domin ta yi bincike.

Sai dai kuma ita EFCC din ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa babu wanda ya cunna ta zuwa binciken wadannan kudade a NNPC.

LAWAN DAURA: Abokin Damo Guza:

Ganin yadda wannan kulli-kurciya ke ta karafkiya, sai nan da nan Shugaban SSS, Lawan Daura ya gaggauta tura jami’an sa domin su hana kama Abba Kyari. Haka wata majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES.

Wannan ne karo na biyu da Lawan Daura ke tura jami’an SSS su hana EFCC kama manyan jami’an gwamnati. Ranar 21 Ga Nuwamba, 2018, SSS sun tari gaban EFCC da fada, inda su ka yi babakere, su ka hana ta kama tsohon shugaban NIA, Ayo Oke da kuma tsohon shugaban hukumar SSS, Ita Ekpeyong.

Defence House: ‘Da Kare Da Biri’ Ta Wallare

Shi dai wannan katafaren wuri ne mai fadin gaske, da ke cikin Maitama, daidai tsallaken mahadar titin kusa da babban ofishin MTN na Abuja. Gidan ya na daya daga cikin gidajen saukar baki na Shugabn Kasa. Shi akan sa Buhari ya zauna cikin sa kafin a rantsar da shi. To a cikin sa ne gidajen Babagana Munguno da na Abba Kyari duk su ke, kuma gidan wannan ya na kallon na wancan.

Dangantaka tsakanin manyan jami’an gwamnatin Buhari biyu, Abba Kyari da Babagana Munguno ba ta da wani armashi ko kadan. Wata majiya ta ce, “su biyun kowa ta ciki na ciki.”

Duk su biyun ’yan kabilar Kanuri ne, ga su kuma su na a kololuwar kusanci da Buahri, sannan kuma ana ganin su biyun ne ke yi wa gwamnatin Buhari kitso-da-kwarkwata.

Artabun SSS Da SOJOJI A Gaban Gidan MUNGUNO

Yayin da jami’an SSS suka bazu birjik a kofar gidan Abba Kyari da ke kusa da gidan Munguno, a safiyar Larabar da ta gabata, wata majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa kowanen su ya rike da makamai.

An ce yayin da Munguno ya fito daga gida ya yi arba da gungun jamai’an SSS, sai ya bata rai, ya kalli hadiman sa a fusace ya ce, “wadancan kuma su wane ne?”

Nan take sai ga mota cike da karta-kartan sojoji, sun yi shirin fada, a bisa umarnin idan sun zo, su karbe bindigogin da ke hannun jami’an SSS.

An ce a nan dai aka yi ta surfa bakaken kalamai a tsakanin jami’an tsaron, daga bisani kuma hankali ya rinjayi fushi, dukkan jami’an su ka fice daga gidan.

MUNGUNO DA KYARI: Me Suka Shaida Wa Buhari?

Wata kwakkwarar majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa washegari ranar Alhamis Shugaba Buhari ya gana da Kyari da kuma Munguno, amma ba a lokaci daya ba. An ce ya gana da su ne domin ya sasanta sabanin da ke tsakanin su.

Wata Sabuwa Inji ’Yan Caca:
A ranar da Buahri ya gana da Munguno da Kyari, sai kuma ga takarda ta fito daga ofshin shugaban kasa ana sanar da cewa an nada Abubakar Rufai Ahmed a matsayin sabon shugaban hukumar tsaro ta NIA.

Rufai Abubakar wani mutum ne da aka tabbatar da cewa ya kware sosai wajen iya magana da yaren Faransa, Turanci da kuma Larabaci fiye da tunanin mai tunani. Ya taba yin aiki a ofishin Majalisar Dinkin Duniya a ofishin ta na Afrika ta Yamma da ke Dakar, babban birnin kasar Senegal.

A bisa dukkan alamu an shiga gaban Munguno, domin an ce akwai wanda ya so a nada shugaban NIA kafin a bai wa Dauda riko, amma sai dai ya ji an nada Dauda ba da sanin sa ko an tuntube shi ba.
An ce shi kan sa Dauda sai dai ya ji labarin an canja shi a kafafen yada labarai.

IBRAHIM MAGU: Kadangaren Bakin Tulu

Babu abin da ake kwana ake tashi da shi a kololuwar tsaron kasar nan, kamar batun Shuagabn EFCC Ibrahim Magu. A lokacin hutun Kirsimeti, an ce Abba Kyari ya ja zugar Ministan Harkokin Cikin Gida, Bello Dambazau, Shugaban SSS, Lawan Daura da kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, inda suka samu Buhari suka ba shi shawarar a canja Magu domin a cewar su, shi ne matsalar da ta hana gwamnatin sa tafiya daidai tare da Majalisar Tarayya. Sun ce saboda Magu ne Majalisar Dattawa ba ta saurin amincewa da batutuwan da shugaban kasa ke kaiwa a gaban ta.

An ce Buhari ya ba su shawara su je su gana da Maiataimakin sa, Osinbajo, domin shi kwararren masanin shari’a ne. Lokacin da su ka samu Osinbajo, ya nuna musu cewa cire Magu zai haifar da matsala, musamman ganin zaben 2019 na karatowa.

Osinbajo ya shaida musu cewa ana cire Magu aka canja shi da wani, to masu bakin magana cewa za su yi batun yaki da cin hanci da rashawa kuma ya zama busar-biri ko shillon-Bilya kenan.

Tags: Abba KyariAbujaBabagana MungunoFannin TsaroHausa AbujaNajeriyaNIAPREMIUM TIMESSSS
Previous Post

‘Yan sandan Kano sun bada belin kwamishinan da ya ce a jefi Kwankwaso

Next Post

Sabbin malaman mu za su fara aiki a Fabrairu – El-Rufai

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Neman suna ne El-Rufai ya yi da maganar Jarabawar malamai amma ba gaskiya bane abin da ya ce- Kungiya Kwadago

Sabbin malaman mu za su fara aiki a Fabrairu - El-Rufai

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda sabon Gwamna ya ƙwato motoci 40 da Matawalle ya yi walle-walle da su
  • ƘARYAR CBN TA ƘARE: Tinubu ya dakatar da Emefiele, gogarman da ya yi wa Naira fentin zabibi, bayan dala ta kai Naira 750 a ƙarƙashin sa
  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.