Kakakin rundunar ‘yan sandar Kaduna Mukhtar Aliyu, ya bayyana cewa rundunar sa za ta ceto sarkin Ikulu Yohanna Kukah da masu garkuwa suka yi garkuwa dashi a garin Ikulu da yamman Talata.
Ya ce duk da cewa masu garkuwan basu kira kowa ba, an baza ‘yan sanda cikin daji domin gano maboyar su.
Yohanna Kukah dan uwan fitaccen shugaban faston Katolika Hassan Kukah ne.
Discussion about this post