• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Digiri Dan-Kwatano, Daga Dr. Ibrahim Siraj

Mohammed LerebyMohammed Lere
January 22, 2018
in Ra'ayi
0
Daukan sabbin ma’aikata: Gwamnati zata dauki masu Diploma, HND

Sanannen abu ne irin tsananin bukatar da dubban matasa ke da ita na shiga manyan makarantu don cigaba da karatunsu bayan kammala karatun sakandare. Wannan bukata ta fi kamari ga jami’o’i wadanda duk shekara su ke fama da adadi mai yawa na masu neman shiga, adadin da nesa ba kusa ba ya zarce abin da za su iya dauka bisa ka’idodi da Hukamar Jami’o’i ta Kasa wato NUC ta dora musu. Lamarin ya na kara tsananta duk shekara sakamakon yawan dalibai masu neman shiga da yake karuwa su kuma jami’o’in ba a fadada su ba ta yadda adadin da za su iya dauke dukkan maneman ba.

Misali, a shekarar da ta gabata kasha talatin bisa dari (30%) ne kawai daga cikin dalibai miliyan daya da dubu dari bakwai (1.7m) da su ka rubuta jarabawar neman shiga jami’o’i wato UTME su ka samu zarafin a dauke su.

Tsananin kwadayin karatu da son sai kowa ya yi aikin gwamnati da kuma gane cewa ba wani ci gaba mai ma’ana da mutum zai iya samu a rayuwarsa idan bai yi karatun ba su ne kanwa uwar gamin hobbasa da farkawar da matasa maza da mata su ka yi don ganin sun zurfafa ilminsu. Wannan hobbasa ta sa shiga jami’a ya zama wani al’amari mai wahalar gaske.

Misali duk dalibin da ya ke nemen shiga jami’a dole ne sai ya tsalleke wasu matakai da su ka hada da samun nasara a jarabawar kammala sakandare (SSCE) da credit biyar da su ka hada da Turanci (English) da Lissafi (Mathematics), samun nasara a jarabawar UTME wacce hukumar JAMB ta ke shiryawa da kuma samun nasara a jarabawar bayan UTME wato Post-UTME da jami’o’i su ke shiryawa. Sai dai abin takaici shi ne duk da wannan wahala babu tabbas cewa dalibi zai samu a dauke shi a makarantar da ya nema ko da ya samu duk nasarar da ake bukata domin akwai yiwuwar a samu adadi mai yawa na wadanda su ka sami irin wannan nasara ko ma wacce ta fi ta kuma jami’o’in ba su da sararin kwashe su duka.

Wannan matsala ta jima ta na ci wa al’umma, musamman gwamnati da iyaye, tuwo a kwarya. A nata bangaren gwamnati ta na ganin ta na yin iya bakin kokarinta wajen fadada jami’o’in da ake da su ta hanyar kara gine-gine don kara karfin abin da su ke iya dauka da kuma samar da sababbi. A zahirin gaskiya kuma a halin yanzu kusan ba wata jiha a Najeriya wacce babu jami’ar gwamnatin tarayya a cikinta. Sannan kusan dukkanin jihohi su na da jami’a mallakin gwamnatin jiha (Kano guda biyu gareta) baya ga dumbin jami’o’i masu zaman kansu da ake ta kafawa musamman a kudancin wannan kasa. Abin tambaya shi ne me yasa duk da wannan fadadawa lamarin kullum ya ke kara kamari? Masana sun yi ittafaki cewa fadadawar da ake samu ko kusa ba ta kai matsayin bukatar da ake da ita ba musamman idan aka kalli irin yadda yawan al’umma ya ke nunnunkawa.

Tuni dai masu hannu da shuni su ka nemawa kansu mafita ta hanyar kai ‘ya’yansu makarantu masu zaman kansu ko dai a nan gida ko kuma a kasashen waje na Turai, Asia kai har ma nan Afurka. Duk da cewa manazarta na ganin cewa tsame ‘ya’yansu da jami’an gwamnati su ke daga jami’o’inmu na gida ya na bayar da gudunmawa ga halin ko-in-kula da ake nunawa ilmi a makarantun gwamnati a wannan kasa, wasu na ganin cewa hakan yana taimakawa wajen rage tsanani akan jami’o’in kuma zai iya samar da dama ga wasu daliban su maye gurabensu. Ko ma dai menene ra’ayin mutum game da wannan, wani abu mai muhimmanci shi ne irin inganci da nagartar karatun da ake yi a kasashen waje. Dole ne a bawa wannan lamari muhimmanci domin daga karshe ko me aka karanto a waje akwai kwakkwaran zaton cewa nan za a dawo a gabatar da shaidar don neman aiki ko wasu bukatu.

A baya-bayan nan akwai rahotanni ma su tayar da hankali da ake samu na bullar wasu makarantu na boge a garin Kwatano (Cotonou) na Jamhuriyar Benin da suke bayar da kwalayen digiri da za ka iya cewa ba su wuce shaidar zur ba ga dalibai musamman daga Nigeria. Akwai abubuwan zargi da tuhuma game da wannan “karatu” na Kwatano, musamman dan takaitaccen lokaci da ake dauka kafin kammalawa. Maimakon shekaru hudu ko biyar ko ma shida na karatu a nan Najeriya a Kwatano dalibi zai iya kammalawa a shakara daya ko biyu.

Har ila yau makarantun su na bayar da dama ga dalibin da ya fara karatu a nan don yin kaura ya koma can ya ci gaba. Wannan ya na bayar da dama ga dalibai da su ka kammala aji daya ko biyu su koma can. Daga cikin rahotanni da ake da su masu dimautarwa akwai daliba da ta kammala shekara daya anan kafin ta koma can sai ga shi shekara daya da rabi bayan komawarta har ta kammala digiri. Akwai dalibi da shi ma da aka kore shi saboda gazawa a daya daga cikin jami’o’in Najeriya, sai ga shi shekara daya da rabi bayan komawar sa irin wadannan jami’o’i na Kwatano har ya kammala karatunsa ya dawo gida da kwalinsa na “digiri”. Misalai irin wadannan su na nan da dama da su ka sa jama’a da dama kokwanto. Anya kuwa! Anya ba lauje cikin nadi? Akwai rahotanni da dama da su ke nuna cewa irin wadannan dalibai su na tarewa ne a guraren sharholiya da shakatawa kuma hakan ba ya hana su sami sakamako mai kyau kwarai da gaske. Shin ya abin ya ke ne?

Ya kamata hukumar NUC ta bincika ta gano hakikanin abin da ya ke faruwa. Menene ingancin wadannan makarantu? Ya ya tsarin karatunsu ya ke? Menene darajar manhajarsu? Wane tsari su ke bi ake kammala karatu da wuri haka? Ya akai daliban da aka san masu rauni ne su ke samun kyakkyawan sakamako cikin dan kankanin lokaci haka? Wanne dabo ko surkelle ake amfani da shi? Shin su na ma amincewa? Ya wajaba gwamanti ta bincika. Idan an tabbatar ba bu wani kaikayi shikenan. Idan an samu coge ko rashin gaskiya dole ne a yi wa al’umma bayani kuma a hana mutanenmu zuwa.

Sannan dole ne a yi watsi da shaidar da aka samo daga wadannan makarantu a lamarin aiki ko takarar siyaya da sauransu. Bai kamata tsananin son digiri ya sa a kyale mutane su dinga bin kowace irin hanya ba. Ba kawai nan ba, akwai makarantu da ake tafiya a wasu kasashe don yi manyan digirori kamar Masters da PhD wadanda su ma akwai zargin cuwa-cuwa a cikinsu. Dole ne NUC ta bincika ta yi wa al’umma bayani.

Babu shakka motoci ‘yan-Kwatano sun taimakawa masu karamin karfi wajen mallakar abin hawa. Amma bai zama dole ne a amince da digiri dan-Kwatano ba domin ilmi daban mota daban.

Dr. Ibrahim Siraj, is from the Department of Mass Communication, Bayero University, Kano. Email: adhamai@yahoo.com, isiraj.mac@buk.edu.ng

Tags: AbujaBUKdigiriHausaKanoKaratuKwatanoLabraiPremium Times Hausa
Previous Post

An sace kannen shugaban karamar hukuma a jihar Neja

Next Post

KIRA GA SHEHU SANI: Ka dawo PDP kawai, ka rabu da APCn nan – Inji Sanata

Mohammed Lere

Mohammed Lere

Next Post
Matsaloli 10 dake tarwatsa hadin kan Najeriya

KIRA GA SHEHU SANI: Ka dawo PDP kawai, ka rabu da APCn nan - Inji Sanata

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna
  • Gwamnatin Tinubu ta sanar da dakatar da harajin (VAT) kan man dizal na tsawon watanni 6
  • Matsayar da aka cimma a taron Gwamnatin Tarayya, NUC da TUC – Minista Idris
  • ‘Gyaran Najeriya sai a hankali, miji na ba da rauhanai ya ke aiki ba’ – Remi Tinubu
  • Ba ni kaɗai ne na fidda sunan Ahmed Lawan ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu ba, akwai wasu da ke bayan fage – Adamu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.