Gwamnatin Kasar Saudiyya ta bayyana cewa zata dawo da gidajen kallo na Sinima a fadin Kasar.
Ministan Al’adu da yada labarai Awwad Alawwad ne ya saka hannu a wannan sanarwa inda ya Kara da cewa yin hakan na daga cikin shirin Kasar na karkata akalar tattalin arzikin Kasar zuwa wasu fannin maimakon dogaro da mai da take yi.
Ya ce za fara aiki da gidajen sinima dinne daga watan Maris din 2018.