Ministan Ilimi Adamu Adamu ya fadi wa manema labarai a fadar gwamnati bayan taron majalisar Zartaswa na wannan mako cewa gwamnati ta amince da kafa wasu sabbin jami’o’i masu zaman kansu a kasar nan.
Jami’o’in da aka amince da su sun hada da Jami’ar Admiralty, Ibusa, Jihar Delta; Jami’ar Spiritan, Nneochi, Jihar Abia; Jami’ar Precious Cornerstone,Jihar Ibadan; Jami’ar koyar da ayyukan asibiti, Pamo, Port Harcourt, Jihar Rivers; Jami’ar Atiba, Jihar Oyo; da jami’ar koyar da ayyukan asibiti, Eko, Jihar Legas.
Discussion about this post