Majalisar dattijai ta lashi takobin magance yawar bazuwa da amfani da miyagun kwayoyi da yazama ruwan dare a kasar nan.
Shugaban majalisar Bukola Saraki ya bayyana haka ne da kakkausar murya a wata ziyara da shugabanin kananan hukumomi, gwamnoni, sarakunan gargajiyya da kungiyoyi masu zaman kansu suka kai masa ofishin sa.
Ya ce majalisar za ta tabbatar ta matsa wa hukumomin da hakkin kamawa da hukunta wadanda aka kama suna aikata haka don ganin an kawo karshen wannan mummunar aiki.
Discussion about this post