Mai ba tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara kan harkar tsaro Sambo Dasuki ya bayyana a Kotu yau domin bada shaida kan shari’ar Olisa Metuh.
Hukumar EFCC ne ta maka Metuh a kotu kan wasu kudade da ya waske da su a lokacin yana kakakin jam’iyyar PDP.
Metuh ya bukaci kotu da ta gaiyaci Dasuki domin bada shaida kan kudin da aka ce an bashi daga kudin siyan makamai.
Discussion about this post