Tsohon gwamnan jihar Legas kuma jigo a jam’iyyar APC ya ce jam’iyyar APC bata yanke shawarar tsayar da Buhari dan takaran shugaban kasa a inuwar jam’iyyar ba.
” Kamar yadda kowa ya sani bamu tsayar da Buhari dan takaran jam’iyyar mu ba. Sannan a sani muna da doka a jam’iyyar mu wanda ya zayyana yadda za a gudanar da zabe da tsayar da dan takara.”
” Babu wani gwamnan da zai fito ya ce ya tsayar da Buhari dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC. Buhari mutum ne mai so abi doka, kuma jam’iyyar mu na da doka, ita za mu bi. Idan ma har muka yadda mu tsayar dashi a matsayin zabin jam’iyya, Ina ganin bamu kauce ma dokar jam’iyya ba sannan bamu saba wa dokar hukumar zabe ba.”
Tinubu ya ce idan ba a manta ba gwamnan jihar Ondo Akeredulu na daga cikin wadanda sukayi wa buhari aiki sannan kuma suka zabe shi a zaben fidda gwani a 2015.
Bayanan da yayi a taron kungiyar kabilar Yarbawa Afenifere da akayi a jihar Ondo, Tinubu ya kara jaddadawa ‘yan kabilar yarbawa cewa za suyi kokarin ganin an ci gaba da samun hadin kan yan kabilar da samar musu ababen more rayuwa.
Discussion about this post