Bayanai da muka samu zuwa yanzu sun nuna cewa sojoji 11 Boko Haram suka kashe a wata harin kwantar bauna da suka kai wa sojojin Najeriya a kauyen Sasawa, dake jihar Yobe.
Bayan haka Kuma Boko Haram sun kwace makamai da abincin da sojojin suke dauke da su.
Irin wadannan hare hare sun fara Zama ruwan dare a wasu yankunan jihar Yobe da Barno a dan kwanakin nan.
Kwanakin baya, irin haka ya auku ga wasu sojojin Najeriya ta irin wannan hari na kwantar bauna inda wasu sojoji hudu suka rasa rayukan su.
Discussion about this post