Rasheed Jimoh-Ijaodola wanda ya kammala babbar digirin sa (doctorate degree) a fannin addinin kiristanci a jami’ar Ilorin ya yi kira ga mutanen duniya da su zauna lafiya da juna.
Ijaodola ya ce ya gano hakan ne yayin da yake karatun sa na babbar digirinsa na uku a adinin kiristanci inda ya yi nazari akan wahayoyin annabawa dake cikin Litafi Mai Tsarki (Holy Bible) wanda ya hada da wahayin Nostradamus.
Ijaodola musulmi ne, farfesan da ya karan ci dokoki kuma shugaban fannin koyar da dokokin na jami’ar Igbinedion dake Okada jihar Edo.
Discussion about this post