TATTALIN ARZIKI
Gwamnati na kokarin ganin ta kara fadada hanyoyin inganta tattalin arziki. Ga tsarin bayar da rance ga manoma, wanda na kaddamar tun 1 Ga Nuwamba, 2015. Shirin kuma ya samu gagarimar nasara, ta hanyar:
1- Raba naira biliyan 43.92 da CBN ta yi ga wasu cibiyoyi 13.
2 – Kananan manoma 200,000 daga jihohi 29 na cin moriyar shirin.
3 – An noma wasu amfanin gona har iri 8 a cikin hekta 233,000. Ana noma shinkafa, alkama, auduga, waken-soya, kiwon kaji, rogo, gyada da kuma noman kifi.
Zan so na yaba wa Gwamnatocin Jihar Kebbi, Legas, Ebonyi da Jigawa dangane da gudummawar su wajen samar da shinkafa da kuma takin zamani.
(Premium Times Hausa) Haka kuma ina jinjina wa Gwamnonin Ondo, Edo, Delta, Imo, Cross River, Ogun, Kaduna da Filato dangane da goyon bayan su ha shirin Shugaban Kasa na inganta noman man ja, roba, kashiw, rogo, tumatir da sauran kayan gona.
Ganin yadda mu ka samu yalwar ruwan sama a wannan damina, harkar noma ta samu wani babban tallafi daga Allah Madaukakin Sarki.
Daga Disamba na shekarar da ta gabata zuwa yanzu, wannan gwamnati ta samar da taki sama da buhuna miliyan 7, kuma ana sayarwa a kan Naira 5,500 kowane buhu mai nauyin 50Kg sabanin yadda farashin yake ada.
Baya ga wannan kuma, Ofishin Shugaban Kasa na kan hanyar fara sabon shirin samar da ayyukan yi har 10,000 ga dimbin matasan mu, ta hanyar sa hannun Babban Bankin Tarayya, CBN.
Harkar samarda hasken wutan lantarki ta zama babbar matsala. Ya zuwa Satumba, 12 ga wata, ya yi karuwar da bai taba yi ba zuwa Megawatts 7,001.(Premium Times Hausa)
Mu na sa ran zai karu zuwa Megawatts 10,0000 nan da shekarar 2020. Ina matukar farin cikin shaida muku cewa Aikin Samar da Hasken Lantarki da sauran nau’ukan Makamashi ya kankama a tsibirin Mambilla.
Idan mu ka sake komawa bangaren tattalin arziki kuwa, watanni bakwai kenan a jere ana samun sassaucin farashin kayayyaki.
Naira ta yi tsayuwar tabarya wuri daya, tun daga Fabrairu zuwa yau, ta na N360 a kowace Dala. Sabanin yadda ta ke N525 a baya.
Yanzu tsarin tattalin arzikin mu ya fitar da mu daga matsalar kuncin tattalin arziki.
Domin kara inganta tafiyar wannan gwamnati, Gwamnatin Tarayya ta na ci gaba da tallafa wa jihohi ta hanyoyin:
1 – Ba su lamuni daga asusun kudaden rarar man fetur.
2 – Tallafa wa hidindimun inganta kasafin kudaden su.
3 – Tallafa musu da kudaden daidaituwar kudaden gudanar da ayyuka wa jihohi da kananan hukumomi.
Gaba gaba daya jimillar kudaden sun kai Naira Tiriyan 1.642.
An yi haka ne domin taimaka wa jihohi su rika biyan albashin baya da ma’aikata ke bi bashi, fansho da sauran kananan ayyuka, wadanda su ka nemi durkushewa a baya.
An kuma kashe naira biliyan 500 wajen ciyar da dalibai, shirin N-Power da kuma shirin samar da muhalli.
Discussion about this post